Aminiya:
2025-07-23@04:55:12 GMT

A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki Sanusi

Published: 22nd, July 2025 GMT

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, ya yi kira da a tsananta hukunci kan masu cin zarafin ’ya’ya mata, yana mai cewa babu wani musulmi nagari da zai yi wa matarsa dukan da har zai yi mata lahani.

A yayin da yake tunatar da malamai da limamai kan muhimmiyar gudunmawar da za su bayar a wannan fage domin yi wa tufkar hanci, Sarkin ya bayyana damuwa kan yadda matsalolin fyade da kuma samun magidantan da ke dukan matansu suka zama ruwan dare a Jihar Kano.

Yunwa na ƙara tsanani a Arewa maso Gabashin Nijeriya — ICRC Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh

Sarki Sanusi na wannan furuci yayin da ya karbi bakuncin tawagar cibiyar bunkasa bincike (dRPC) da kuma cibiyar nazarin addinin musulunci ta Jami’ar Bayero da ke Kano (CCID) suka kai ziyara fadarsa ta Gidan Rumfa a birnin Dabo.

A cewar Sarkin, “ban zan taba goyon dukan mace ba, kuma duk masu yi, suna yi ba da niyyar ladabtarwa ba. Amma abin takaicin da muke gani a yau shi ne yadda ake yi wa mata jina-jina da sunan ladabtarwa.

“Musulunci yana fifita mata da daraja fiye da kowane addini kuma duk masu neman fakewa a karkashinsa don cin zarafinsu, ba su ma fahimci addinin ba.

“Duk wanda yake dukan matarsa har ya yi mata rauni ba mutumin kirki ba ne, kuma ba ni na fadi haka ba, Annabi Muhammad (SAW) ne ya fada, wadanda ba su karanta ba ne ba su sani ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Sarki Muhammadu Sanusi II

এছাড়াও পড়ুন:

Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano

Mazauna unguwar Zangon Kaya da ke karamar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano sun shiga cikin makoki sakamakon nutsewar da wasu matasa hudu suka yi a hanyar ruwa da baraguzan gine-gine suka tushe.

 

Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Yusif, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin.

 

A cewarsa, lamarin ya faru ne bayan wadanda lamarin ya rutsa da su suka shiga mashigar ruwa da suka taru sakamakon toshewar hanyar jirgin da ake yi.

 

Ya kara da cewa, kamar yadda shaidun gani da ido suka bayyana, da farko biyu daga cikin wadanda abin ya shafa sun shiga cikin ruwan da nufin yin iyo amma sun makale. A kokarin ceto su, mutum na uku ya shiga, shi ma ya makale. Abin baƙin ciki, mutum na huɗu, yana ƙoƙari ya ceci sauran, ya fuskanci irin wannan matsalar.

 

Saminu ya yi nuni da cewa, kafin isowar hukumar kashe gobara mazauna yankin sun yi nasarar ceto biyu daga cikin wadanda abin ya shafa. Yayinda “Sauran biyun, tawagar ceto ta fito da

 

Wadanda abin ya shafa sun hada da Nasirudden Tasi’u dan shekara 25 da Basir Sani mai shekaru 28 da Yakubu Muhd dan shekara 22 da Usman Ubale dan shekara 26.

 

Jami’in hulda da jama’a ya yi nuni da cewa, an samu dukkanin mutane hudun a sume kuma daga baya aka tabbatar da sun mutu.

 

“An mika gawar su ga SP Abdulkadir M. Albasu na sashin ‘yan sanda na Dawanau domin ci gaba da bincike”.

 

Saminu ya ce, Daraktan hukumar kashe gobara ta jiha Alhaji Sani Anas ya jajantawa iyalan mamatan.

 

Ya kuma gargadi jama’a da su guji shiga cikin ruwa ba tare da izini ba ko kuma masu hadari, musamman wadanda ayyukan gine-gine ya shafa.

 

“Muna kira ga ‘yan ƙasa da su guji yin iyo ko wasa a cikin kududdufi, musamman waɗanda aka toshe ko ba a tsara su don amfani da nishaɗi ba.

 

Al’umma na ci gaba da nuna alhininsu yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kan al’amuran da suka dabaibaye wannan mummunan lamari.

 

Rel/Khadijah Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
  • Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
  • NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa
  • A binciko mesar da ta ɓace a Kano — Sanusi II
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Maida Gidan Marayu Zuwa Cibiyar Gyaran Mata Masu Shaye
  • Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar