A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki Sanusi
Published: 22nd, July 2025 GMT
Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, ya yi kira da a tsananta hukunci kan masu cin zarafin ’ya’ya mata, yana mai cewa babu wani musulmi nagari da zai yi wa matarsa dukan da har zai yi mata lahani.
A yayin da yake tunatar da malamai da limamai kan muhimmiyar gudunmawar da za su bayar a wannan fage domin yi wa tufkar hanci, Sarkin ya bayyana damuwa kan yadda matsalolin fyade da kuma samun magidantan da ke dukan matansu suka zama ruwan dare a Jihar Kano.
Sarki Sanusi na wannan furuci yayin da ya karbi bakuncin tawagar cibiyar bunkasa bincike (dRPC) da kuma cibiyar nazarin addinin musulunci ta Jami’ar Bayero da ke Kano (CCID) suka kai ziyara fadarsa ta Gidan Rumfa a birnin Dabo.
A cewar Sarkin, “ban zan taba goyon dukan mace ba, kuma duk masu yi, suna yi ba da niyyar ladabtarwa ba. Amma abin takaicin da muke gani a yau shi ne yadda ake yi wa mata jina-jina da sunan ladabtarwa.
“Musulunci yana fifita mata da daraja fiye da kowane addini kuma duk masu neman fakewa a karkashinsa don cin zarafinsu, ba su ma fahimci addinin ba.
“Duk wanda yake dukan matarsa har ya yi mata rauni ba mutumin kirki ba ne, kuma ba ni na fadi haka ba, Annabi Muhammad (SAW) ne ya fada, wadanda ba su karanta ba ne ba su sani ba.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano Sarki Muhammadu Sanusi II
এছাড়াও পড়ুন:
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.
An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.
Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.
An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.
Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.
Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp