Yunwa na ƙara tsanani a Arewa maso Gabashin Nijeriya — ICRC
Published: 22nd, July 2025 GMT
Kungiyar Agaji ta Red Cross (ICRC) ta bayyana cewa yunwa na ƙara tsananta a Arewa maso Gabashin Nijeriya, musamman a jihohin Borno, Adamawa da Yobe.
A cewar rahoton, rikicin da ya dauki shekaru 16 ya durƙusar da kasuwanci da hanyoyin samun aiki, wanda hakan ya tilastawa mutane dogaro da ƙananan gonaki don rayuwa.
ICRC ta bayyana cewa fiye da mutum miliyan 3.7, wadanda galibi manoma ne na fuskantar barazanar matsanancin rashin abinci a yankin da aka shafe shekaru ana rikici.
Churi Ibrahim, wani tsohon manomi dan shekara 70 da ke ciyar da iyalinsa goma, ya ce farashin abinci ya yi tashin gwauron zabi, kuma kudin ɗinki da yake samu da dare bai isansu.
Modu Umar, wani shugaban al’umma, ya bayyana cewa yunwa tana haddasa cututtuka kamar gudawa a cikin yara da manya saboda rashin abinci da magani.
“Mutane na fita nesa su tara itace domin samun kudin siyan abinci,” in ji shi.
ICRC dai ta ce ta fara wani shiri na taimaka wa noma ta hanyar raba iri da kayan aikin noma ga sama da iyalai 21,000 a bana, domin tallafa musu a lokutan kaka da rani.
“Ana kuma shirin rarraba famfunan ban-ruwa masu aiki da hasken rana domin noman rani,” in ji ƙungiyar ICRC.
Shugabar ofishin ICRC a Maiduguri, Diana Japaridze, ta ce ana fargabar za a fuskanci matsanancin ƙarancin abinci daga Yuli zuwa Satumba, inda mutane ke buƙatar sayen abinci, amma ƙarancin kudi yana hana su cika buƙata.
A cewarta, matsananciyar yunwar na janyo tsamurewar jiki saboda rashin abinci mai gina jiki musamman a tsakanin ƙananan yara ’yan ƙasa da shekaru biyar da kuma mata masu shayarwa.
Ƙungiyar ICRC na aiki a Borno tun 2012 inda take taimaka wa al’ummomin da rikici ya shafa da kuma kare martabar fararen hula bisa dokokin Geneva na 1949.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas jihar Borno Nijeriya yunwa
এছাড়াও পড়ুন:
Libya Ta Tasa Keyar Baƙin Haure Yan Kasar Sudan 700 Zuwa Kasarsu
Gwamnatin Libya ta tasa keya daruruwan baƙin haure ‘yan ƙasar Sudan 700 zuwa ƙasarsu da yaƙi ya ɗaiɗaita, A cewar mahukuntan, waɗannan mutanen sun yi hijira zuwa Libya ne domin gujewa yaƙi da talauci, inda suke neman hanyar tsallakawa zuwa Turai.
A cewar huƙumar kula da baƙin haure, an kori mutane 700 daga Libya da aka kama a tsakiya da kudu maso gabashin ƙasar, inda aka tura su zuwa Sudan a ranar Juma’ar da ta gabata ta ƙasa.
Bayanin ya nuna cewa wasu daga cikin waɗanda aka korar na ɗauke da cututtuka masu yaɗuwa kamar su hepatitis da cuta mai karya garkuwar jiki, wasu kuma an tura su ne saboda laifuffuka ko kuma dalilan tsaro.
Korar ta zo ne a lokacin da mahuƙuntan ke ci gaba da yaƙi da safarar mutane a gabashin Libya, wanda ke ƙarƙashin ikon kwamandan sojoji Khalifa Hiftar.
A makon da ya gabata, masu tsaron gaɓar teku a gabashin Libya sun kame wani jirgin ruwa da ke ɗauke da baƙin haure 80 da ke neman zuwa ƙasashen ƙetare, a gabashin birnin Tobruk.
Yaƙin da hukumomin ke yi sun haɗa da kai hare-hare kan wuraren da ake safarar mutane a gabashi da kudancin Libya. A farkon wannan watan, an ƙwato baƙin haure ‘yan Sudan 104, ciki har da mata da yara, da aka tsare a gidan da ake tara mutane da ake fataucin su a birnin Ajdabiya, mai nisan kilomita 800 daga babban birnin Tripoli, a cewar ƴan sa kai na yankin.
Libya ta zama hanyar wucewa ga mutanen da ke guje wa yaƙi da talauci a yankunan gabas ta tsakiya da Afirka, inda suke neman rayuwa mai kyau a Turai.
Masu safarar mutane sun ci gajiyar rashin kwanciyar hankali a Libya tsawon shekaru goma, inda suke shigar da baƙin haure ta iyakokin ƙasar da suka haɗa da ƙasashen Chadi da Nijar da Sudan da Masar da Aljeriya da kuma Tunisiya.