HausaTv:
2025-07-23@10:47:28 GMT

 Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba

Published: 22nd, July 2025 GMT

Fira ministan HKI wanda kotun duniya ta manyan laifuka take nem ruwa a jallo ya bayyana cewa; Babu yadda za su tsayar da yakin Gaza, matukar kungiyar Hamas ba ta mika wuya baki day aba.

Benjemine Netanyahu ya kuma ce; A lokacin da Hamas za ta mika makamanta ne, shi ne za mu yi tunanin ko za mu bude mata hanyar ficewa daga Gaza, da kuma dakatar da yaki.

A gefe daya tashar talabijin din CNN ta ambato wata majiya ta gwamnatin Amurka tana cewa; Amurka ta gargadi kungiyar Hamas akan cewa, hakurinta ya kusa karewa akan batun tsagaita wuta, tare da neman kungiyar ta gwagwarmaya ta bayar da jawabi a cikin gaggawa kafin makwanni biyu masu zuwa.

Tashar talabijin din CNN din ta kuma bayyana cewa;  Amurkan ta bai wa Hamas lamunin cewa Isra’ila ba za ta shiga cikin tattaunawar kawo karshen yaki ba a tsawon lokacin dakatar da yaki da zai dauki kwanaki 60.

Sai dai kuma majiyar ta fada wa tashar talabijin din CNN cewa, Amurkan za ya janye wannan lamunin idan har kungiyar ta Hamas ba bayar da jawabi a cikin sauri ba.

 Sai dai kuma masu bin diddigin abubuwan da suke faruwa sun bayyana cewa; HKI ce ummul-haba’isin tsaikon da ake samu a tsagaita wutar yakin ba kungiyar gwgawarmaya ta Hamas ba.

A nata gefen kungiyar Hamas ta ce, a mataki na baidaya kungiyar tana son ganin an tsagaita wuta, duk da cewa jagorancin kungiyar na Gaza ne zai yanke hukunci na karshe.Khalilul Hayya wanda ya bayyana hakan ya kara da cewa; Jagororin Hamas na cikin gida ne ke da alhakin aiwatar da duk wani mataki na tsagaita wuta, don haka su ne za su bayyana mataki na karshe.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tsoffin Jami’an ‘Yan Sanda Sun Bukaci A fitar Da Su Daga Cikin Shirin Fansho

Jami’an ‘yan sanda da suka yi ritaya a jihar Kwara sun gudanar da zanga-zangar lumana don neman a cire su daga shirin bayar da gudunmawar fansho (CPS).

 

An ga jami’an ‘yan sandan da suka yi ritaya a jihar karkashin kungiyar ‘yan sandan Najeriya mai ritaya (ARPON), dauke da kwalaye masu rubuce-rubuce daban-daban kamar su “Shugaban kasa, NASS da IGP ya kamata a girmama ‘yan sanda su kebe ‘yan sanda daga CPS, su kafa hukumar ‘yan sanda ta fensho don gudanar da gratuity da fansho, idan CPS na da kyau haka, me ya sa AIGs da sauran su suka fice daga cikin shirin?

 

Da yake jawabi ga ‘ya’yan kungiyar a lokacin zanga-zangar lumana a Ilorin, shugaban kungiyar, Yakubu Jimoh, babban Sufeton ‘yan sanda mai ritaya, ya yi zargin cewa shirin yana cike da kalubale tun farkonsa.

 

A cewarsa jami’an da suka yi ritaya wadanda suka fada cikin tsarin fansho ya kamata a kebe su kamar wadanda suka kai matsayin Janar a rundunar.

 

Ya nemi kafa hukumar fansho ta ‘yan sanda mai alhakin kula da al’amuran ‘yan sanda na fansho kamar yadda ya shafi sauran hukumomin tsaro.

 

Jimoh ya bayyana cewa rahoton kwamitin majalisar dattijai mai kula da kafa da ayyukan gwamnati a kan kudirin dokar kafa hukumar fansho ta ‘yan sanda, wadda aka gudanar a watan Nuwambar bara ta fitar da shi, duk da cewa an gudanar da shi watanni takwas da suka gabata.

Ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da majalisar dokokin kasar da su gaggauta bin diddigin yadda majalisar za ta bi wajen fitar da naira biliyan 758, karancin kudaden fansho da ke bin hukumomin tsaro.

 

A nasa bangaren, mashawarcin shari’a na kungiyar ‘yan sandan Najeriya mai ritaya Adekunle Iwalaiye, ya ce jami’an da suka yi ritaya sun cancanci a biya su fansho na rayuwa ba wai dan abin da ake jefa musu ba duk wata ba.

 

Ya bukaci gwamnati da ta yi aiki da bukatar wadanda suka yi ritaya, duba da irin ayyukan alheri da suka yi wa kasar nan tsawon shekaru 35.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Eritrea ta gargadi Habasha game da yunkurin kafa tashar jiragen ruwa a cikin yankinta
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  • Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21
  • Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 
  • Kamfanonin lantarki ya zu katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 
  • Tsoffin Jami’an ‘Yan Sanda Sun Bukaci A fitar Da Su Daga Cikin Shirin Fansho
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi