Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba
Published: 22nd, July 2025 GMT
Fira ministan HKI wanda kotun duniya ta manyan laifuka take nem ruwa a jallo ya bayyana cewa; Babu yadda za su tsayar da yakin Gaza, matukar kungiyar Hamas ba ta mika wuya baki day aba.
Benjemine Netanyahu ya kuma ce; A lokacin da Hamas za ta mika makamanta ne, shi ne za mu yi tunanin ko za mu bude mata hanyar ficewa daga Gaza, da kuma dakatar da yaki.
A gefe daya tashar talabijin din CNN ta ambato wata majiya ta gwamnatin Amurka tana cewa; Amurka ta gargadi kungiyar Hamas akan cewa, hakurinta ya kusa karewa akan batun tsagaita wuta, tare da neman kungiyar ta gwagwarmaya ta bayar da jawabi a cikin gaggawa kafin makwanni biyu masu zuwa.
Tashar talabijin din CNN din ta kuma bayyana cewa; Amurkan ta bai wa Hamas lamunin cewa Isra’ila ba za ta shiga cikin tattaunawar kawo karshen yaki ba a tsawon lokacin dakatar da yaki da zai dauki kwanaki 60.
Sai dai kuma majiyar ta fada wa tashar talabijin din CNN cewa, Amurkan za ya janye wannan lamunin idan har kungiyar ta Hamas ba bayar da jawabi a cikin sauri ba.
Sai dai kuma masu bin diddigin abubuwan da suke faruwa sun bayyana cewa; HKI ce ummul-haba’isin tsaikon da ake samu a tsagaita wutar yakin ba kungiyar gwgawarmaya ta Hamas ba.
A nata gefen kungiyar Hamas ta ce, a mataki na baidaya kungiyar tana son ganin an tsagaita wuta, duk da cewa jagorancin kungiyar na Gaza ne zai yanke hukunci na karshe.Khalilul Hayya wanda ya bayyana hakan ya kara da cewa; Jagororin Hamas na cikin gida ne ke da alhakin aiwatar da duk wani mataki na tsagaita wuta, don haka su ne za su bayyana mataki na karshe.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Haka kuma, wannan na faruwa ne makonni biyu bayan yin garkuwa da Pastor Friday Adehi na Christian Evangelical Fellowship of Nigeria (CEFN) tare da wani abokin cocinsa bayan kammala wa’azi. Wannan ya kara nuna yadda matsalar garkuwa ke ta’azzara a yankin Kogi East.
A gefe guda, kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA), reshen Idah, ta bukaci gwamnati a matakai daban-daban da ta dauki matakan gaggawa don kawo karshen satar mutane a jihar. Shugaban kungiyar, Barr. James Michael, ya ce yawaitar garkuwa a kan titunan yankin ya jefa rayukan jama’a cikin hatsari, don haka gwamnati ya kamata ta dauki tsauraran matakai domin kare lafiyar al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp