HausaTv:
2025-06-06@14:52:12 GMT

Trump ya haramtawa ‘yan kasashen duniya 12 shiga Amurka

Published: 5th, June 2025 GMT

Shugaba Donald Trump na Amurka ya haramtawa kasashen duniya 12 shiga Amurka a wani mataki da ya ce na kare kasar ne daga “yan ta’adda na kasashen waje.

Wata takarda da fadar White House ta fitar a ranar Laraba ta ce haramcin, wanda zai fara aiki daga ranar 9 ga watan Yuni, ya shafi kasashen Afghanistan, Burma, Chadi, Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo, Equatorial Guinea, Eritrea, Haiti, Iran, Libya, Somalia, Sudan, da kuma Yemen.

Baya ga hakan akwai wasu kasashe bakwai su ma da aka gindawa wasu sharudda da suka hada da Burundi, Cuba, Laos, Saliyo, Togo, Turkmenistan da kuma Venezuela.

A cewar Amurka matakin bai shafi mutanen da balaguron su zuwa kasar ke da amfani ga muradun kasar ba.”

Haka ma  ‘Yan wasan kwallon kafa da za su fafata a gasar cin kofin duniya ta 2026, da za a gudanar a Amurka, Mexico da Canada, da kuma ‘yan wasa a gasar Olympics ta Los Angeles ta 2028, takunkumin ba zai shafe su ba.

Matakin dai na da nasaba ne da harin da aka kai a Colorado, in ji Donald Trump.

A ranar Lahadi, data gabata ce, wani mutum ya jefa abubuwa masu tayar da wuta a kan mahalarta tattakin mako-mako a jihar Colorado na nuna goyon baya ga ‘yan Isra’ila da ake garkuwa da su a zirin Gaza.

A cewar fadar White House, wanda ake zargi da kai harin ya shiga a Amurka ne “ba bisa ka’ida ba.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kotun ICC Ta Yi Tir Da Amurka Saboda Takunkuman Da Ta Dorawa Alkalan Kotun Don Hanata Aikinta Da Yenci

Kotun kasa da kasa ta ICC ta yi tir da gwamnatin kasar Amurka wacce ta kakabawa al-kalan kotun guda hudu saboda hannu da suke da shi wajen fidda sammacin kama fray ministan HKI Benyamin Natanyahu.

Kotun ta kara da cewa tana goyon bayan alkalanta kuma zata ci gaba da aikinta na tabbatar da adalci a duniya duk tare da abinda suke faskanta. Kotun ta bayyana cewa tana aikinta ne bisa goyon bayan kasashen duniya 125 wadanda suka fito daga dukkan kusruwowin duniya.

Takunkuman dai ya shafi wadannan alkalai su 4 kuma mata. Kuma sun hana ko wanne daga cikinsu, shiga kasar Amurka kuma idan suna da kadarori ko kudade gwamnatin Amurka ta kwace su.

A cikin watan Nuwamban shekara ta 2024 ne dai kotun ta ICC wacce take zama a birnin Haque ta fidda sammacin kama Firay ministan HKI Benyamin Natanyahu da kuma tsohon ministan yakin kasar Yoav Galant saboda zargin aikata laifukan yaki a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miliyoyim Musulmi A Nan Iran Da Sauran kasashen Duniya Ne Suka Yi Sallar Idin Layyah
  • Kotun ICC Ta Yi Tir Da Amurka Saboda Takunkuman Da Ta Dorawa Alkalan Kotun Don Hanata Aikinta Da Yenci
  • Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
  • Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 
  • Qolibuf: Kungiyar BRICS Dama Ci Ta Kauda Danniyar Amurka A Kan Kudaden Kasashen Duniya
  • Maniyyata na hawan Arfa a kasar Saudiyya
  • Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
  • Babban Zauren MDD Ta Zabi Kasashen Congo Da Liberian Na Zama Mambobi A Kwamitin Tsaro
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi