Aminiya:
2025-07-11@22:13:11 GMT

Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda

Published: 11th, July 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta bayyana dalilin da ya sa ta gayyaci malamin addini Sheikh Lawal Triumph.

A wata sanarwa da ta fitar, ’yan sanda sun ce sun sani cewa wasu daga cikin wa’azozin da Sheikh Triumph ke yi suna haddasa rashin jituwa a tsakanin al’ummar jihar.

Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote

Rundunar ta ce kowa na da ’yancin faɗin albarkacin bakinsa, amma dole ne komai ya kasance bisa doka.

Saboda haka ne Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, ya gayyaci Sheikh Lawal Triumph don tattaunawa da jami’an gwamnati, shugabannin addini da na al’umma.

Manufar ita ce a nemi hanyar hana irin wannan rikici sake faruwa a nan gaba.

Rundunar ta kuma buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu su guji yin abubuwan da za su haifar da tashin hankali.

“Yana da muhimmanci a girmama ra’ayin juna da abin da mutane suka gaskata, kuma a tabbatar da cewa duk abin da mutum zai faɗa ko zai yi bai saɓa wa doka ba,” in ji rundunar.

Wannan lamari ya fara ne bayan wani wa’azi da Sheikh Lawal Triumph ya yi, wanda ya tayar da ƙura.

Ya faɗi haka ne a matsayin martani ga waɗanda suke musanta wani hadisi da ke cewa kwarkwata ƙazanta ce.

Wannan ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda wasu suka fara kiran a kashe Sheikh Lawal Triumph bisa zargin ya yi izgili ya Manzon Allah (S.A.W).

Rundunar ta kuma shawarci jama’a da su kai koken su ga hukumomin da suka dace, maimakon yaɗa saƙonni da za su iya tayar da hankali a shafukan sada zumunta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Sheikh Lawal Triumph Wa azi Sheikh Lawal Triumph

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Kwamandan Sojin Iran Ya Bayyana Cewa Iran Ta Koyawa Gwamnatin Isra’ila Hankali

Manjo Janar Hatami: Nasarar da gwamnatin Musulunci ta samu kan makiya yahudawan sahayoniyya wata babbar nasara ce ga al’ummar Iran

Babban kwamandan sojojin kasar Iran Manjo Janar Amir Hatami ya bayyana cewa: Dakarun tsaron sama na sojojin Iran sun cimma wani gagarumar nasara a yakin da suka yi da makiya yahudawan sahayoniyya.

A wata ganawa da iyalan shahidi Kanar Bostan Afrouz, Manjo Janar Hatami ya kara da cewa: Makiya sun kasa cimma tsare-tsare da shirye-shiryensu da suka rigaya sukaaniyar cimmawa, kuma sun fuskanci mummunar martani da shan kashi.

Ya ci gaba da cewa: Nasarar da gwamnatin Musulunci ta samu kan makiya yahudawan sahayoniyya duk da karfin soja da kudi da suke da su, baya ga bayanan sirri da suke tabbatar da samun goyon bayan gwamnatin kama karyar Amurka, wata babbar nasara ce ga al’ummar Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tsare mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Kotu ta aike mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 24 a Arewa maso Gabashin Nijeriya
  • ’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano
  • ’Yan sanda sun ƙaddamar da samamen “Operation Kukan Kura”, sun kama mutum 98 a Kano
  • Babban Kwamandan Sojin Iran Ya Bayyana Cewa Iran Ta Koyawa Gwamnatin Isra’ila Hankali
  • Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal
  • Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
  • Na Biya Dukkanin Bashin Da ‘Yan Fansho Ke Bin Zamfara- gwamna Lawal