HausaTv:
2025-07-11@22:25:07 GMT

An Kashe Jami’in Sojan HKI A Gaza

Published: 11th, July 2025 GMT

Rundunar sojan mamaya ta sanar da kashe  daya daga cikin jami’an sojojinta dake karkashin rundunar “Golani” a yankin Khan-Yunus dake Gaza.

Da safiyar yau Juma’a ne dai sojojin mamayar HKI su ka snar da cewa wani daga cikin mayakansu mai mukamin  Captain ya halaka a Gaza, kuma tuni sun bude bincike akan abinda ya faru.

Rahoton tashar talabijin din ” Cane” ta HKI ya ambaci cewa, sojan da aka kashe yana cikin wadanda su ka kai hari a garin Khan-Yunus a jiya Alhamis.

Sojojin mamaya sun kai hari ne a cikin wani gida a ci gaba da kashe ‘yan gwgawarmaya da suke yi, sai dai ginin gidan ya rufta da su, bayan da nakiyar da take cikinsa ta fashe.

Tun a jiya Alhamis ne dai kafafen watsa labarun na HKI su ka fara Magana akan cewa sojojin da suke Gaza, suna fuskantar yanaki mai tsanani, da hakan yake nufin cewa an halaka wani adadi nasu.

An ga jirgin sama mai saukar angulu yana shawagi a yankin da aka yi kazamin fada a tsakanin ‘yan gwgawarmaya da kuma sojojin mamaya.

A cikin kwanakin bayan nan dai ‘yan gwgawarmaya suna kara samun nasarar halaka sojojin HKI da suke yi wa al’ummar yankin kisan kiyashi da kuma jikkata wani adadi mai yawa nasu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno

Dakarun sojojin Nijeriya na rundunar sojojin sama tare da haɗin gwiwar Operation Haɗin Kai sun kai farmaki kan wasu muhimman wuraren da ’yan ta’adda suka mamaye a tsaunin Mandara da ke Jihar Borno.

An samu labarin cewa rundunar sojin sama ta gudanar da samamen ta ne a wani wuri da aka san shi da tudu mai tsauni, wanda ke kan iyakar Nijeriya da Kamaru, bayan samun bayanan sirri.

An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos ’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano

Daily Trust ta ruwaito cewa, samamen share fagen ya zo ne ƙasa da sa’o’i 24 da shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya umurci sojoji da su kawar da duk maƙiya da ke barazana a ƙasar nan.

Kakakin rundunar sojin sama na Nijeriya, Ehimen Ejodame ya shaidawa manema labarai a Abuja cewa, aikin sa ido da binciken da sojojin ke yi ya ba da alamun cewa maharan na shirin kai hare-hare.

Air Commodore, Ejodame ya yi bayanin cewa matsugunin da suke amfani da shi mai amfani da lantarki da na’urar hasken rana da baƙaƙen tutoci, alama ce ta sake farfaɗowar maharan a wurin kafin a kai musu harin bam a tarwatsa su.

A cewarsa, manyan samamen, Wa Jahode da Loghpere, sun daɗe suna zama mafaka ga Ƙungiyar Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal-Jihad (JAS), ɓangaren ’yan Boko Haram da ke da matsuninsu a can.

Ya ce, baya ga yadda aka tarwatsa matsunin ta sama da ya lalata kayan aikin ‘yan ta’addar, an kashe da dama daga cikinsu ciki har da kwamandojin su a harin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara
  • Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Zagaye na 5 A Tattaunawar Gaza da HKI  Ya tashi ba tare da Sun Dai-daita ba A Doha
  • Trump Ya Kakabawa Wata Jami’in MDD Takunkumi Bayan Ta Fallasa Laifukan HKI Da Hannun Amurka A Ciki
  • Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 30 a Katsina
  • HKI: Sojoji 62 Ne Su Ka Halaka A Gaza A Cikin Wannan Shekara Ta 2025
  • Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki
  • HKI Ta Kashe Falasdianwa 6 A Gaza, Kuma Tsoffin Fursinoni