Rundunar sojan mamaya ta sanar da kashe daya daga cikin jami’an sojojinta dake karkashin rundunar “Golani” a yankin Khan-Yunus dake Gaza.
Da safiyar yau Juma’a ne dai sojojin mamayar HKI su ka snar da cewa wani daga cikin mayakansu mai mukamin Captain ya halaka a Gaza, kuma tuni sun bude bincike akan abinda ya faru.
Rahoton tashar talabijin din ” Cane” ta HKI ya ambaci cewa, sojan da aka kashe yana cikin wadanda su ka kai hari a garin Khan-Yunus a jiya Alhamis.
Sojojin mamaya sun kai hari ne a cikin wani gida a ci gaba da kashe ‘yan gwgawarmaya da suke yi, sai dai ginin gidan ya rufta da su, bayan da nakiyar da take cikinsa ta fashe.
Tun a jiya Alhamis ne dai kafafen watsa labarun na HKI su ka fara Magana akan cewa sojojin da suke Gaza, suna fuskantar yanaki mai tsanani, da hakan yake nufin cewa an halaka wani adadi nasu.
An ga jirgin sama mai saukar angulu yana shawagi a yankin da aka yi kazamin fada a tsakanin ‘yan gwgawarmaya da kuma sojojin mamaya.
A cikin kwanakin bayan nan dai ‘yan gwgawarmaya suna kara samun nasarar halaka sojojin HKI da suke yi wa al’ummar yankin kisan kiyashi da kuma jikkata wani adadi mai yawa nasu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Adadin Falasdinawan Da Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Sun Haura 100
Hukumar agaji a yankin Gaza ta sanar da cewa fiye da mutane 100 ne su ka yi shahada.
Hukumar ta agaji ta bayyana abinda HKI take yi na ci gaba da kai wa Gaza hare-hare a matsayin keta tsagaita wuta. Su kuwa kungiyoyin gwgawarmaya a yankin sun bayyana abinda yake faruwwa da cewa yana da hatsarin gaske.
Ma’aikatar kiwon lafiya a yankin Gaza, ta sanar da cewa; a cikin shahidan da akwai kananan yara 46, sai kuma wasu 253 da su ka jikkata.
Asibitin “ Nasir” ya sanar da cewa wasu mutane 20 sun yi shahada sanadiyyar hare-haren sojojin HKI a birnin Khan-Yunus dake kudancin birnin Gaza.
Wasu jerin hare-haren ‘yan sahayoniyar sun shafi gidajen mutane a Khan-Yunus da Deir-Balah da Gaza. Sun kuwa yi amfani ne da jiragen sama marasa matuki wajen kai hare-haren. An sami shahidai 3, a yankin sai kuma wasu Karin shahidan 4 sansanin ‘yan hijira dake “Ardh-Insan” a gabas da asibitin Aqsa dake Deir-Balah.
Sojojin HKI sun kuma kai wani hari da jirgin sama maras matuki akan sansnain ‘yan hijira a dandalin garin Deir-Balah da ya ci rayukan falasdinawa 4. A yankin al-mawasi dake yammacin Khan-Yunus, wasu Faalsdinawan 5 sun yi shahada.
A baya kadan, ofishin hukumar Gaza ya sanar da cewa sau 127 HKI ta keta yarjejeniyar tsagaita wutar yaki, wacce ta fara aiki a ranar 10 ga watan nan na Oktoba mai karewa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka Ta Hana Marubuci Dan Nigeria Wole Soyinka Izinin Shiga Amurka October 30, 2025 Pakistan Tayi Barazanar Daukar Mataki Bayan Rushewar Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta Da Afghanistan. October 29, 2025 IRS: Sanya Sabbin Takunkumi Kan Kasar Iran Zai Haifar Da Mummunan Sakamakon A Yankin October 29, 2025 An saka dokar Ta Baci Bayan Barkewar Zanga-zanga A Zaben Shugaban Kasar Tanzaniya October 29, 2025 Majalisar Dattawa A Najeriya Ta Tantance Sabbin Manyan Hafsoshin Sojin Kasar October 29, 2025 Shugaban kasar Iran Ya Taya Takwaransa Na Turkiya Murnar Zayowar Ranar Samun Yancin Kai October 29, 2025 Bayan Kwace Birnin Al-Fasher Kungiyar Rapid Support Forces Suna Ci Zarafin Al’Umma October 29, 2025 Iran Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Ake Kaiwa Fararen Hula A Birnin El-Fasher Na Sudan October 29, 2025 Jakadan Iran A MDD Ya Jaddada Kawo Karshen Takunkumin Amurka Kan Kasar Cuba October 29, 2025 Jami’ar MDD Ta Musamman A Falasdinu Ta Soki Shirin Trump Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci