Kwamatin kananan hukumomi na Majalisar Dokokin jihar Jigawa ya duba ayyukan raya kasa da karamar hukumar Kirikasamma ta samu nasarar gudanarwa daga watan Oktobar 2024 kawo yanzu.

Shugaban Kwamatin, Alhaji Aminu Zakari, ya kafa kananan kwamitoci guda biyu domin samun nasarar tantance ayyukan a cikin garin   Kirikasamma da kauyuka.

Karamin Kwamati na daya bisa jagorancin wakilin mazabar
Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashimu Kanya, ya duba aikin sanya soma da tona riniyar tuka tuka a mayanka da magudanin ruwa a garin Marma da aikin gina rumfunan kasuwa a garuruwan Tasheguwa, Marma, Dilmari da Madaci.

Alhaji Ibrahim Hashim Kanya ya bayyana wa shugaban kamsilolin karamar hukumar wanda ke yiwa tawagar rakiya, Malam Isyaku Abdullahi, muhimmancin ziyarar duba ayyukan Gwamnati dan tabbatar da inganci.

Sai Kuma karamin Kwamati na biyu bisa jagorancin wakilin mazabar Kiyawa Alhaji Yahaya Muhammad Andaza wanda ya duba aikin gyaran hanyar Gafta zuwa Baturiya akan fiye da naira milyan 4 da dubu dari 2, wadda ambaliyar ruwa ta lalata a daminar bara da kuma aikin gina rumfar kasuwa a garin Baturiya.

Tun da farko a sakatariyar karamar hukumar Kirikasamma, Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa Kuma wakilin mazabar Gwiwa,
Alhaji Aminu Zakari ya ce ziyarar Kwamatin na daga nauyin da tsarin mulki ya dorawa bangaren majalisa wajen duba manufofi da shiryeyen Gwamnati baya da yin doka da amincewa da kasafin kudin kowacce shekara.

Alhaji Aminu Zakari ya ce Kwamatin Yana duba kundin bayanan harkokin Kudi da na sha’anin Mulki da su ka hadar da littafin shiga da fitar kudade da takardun biyan kudade na voucher da alkaluman tattara kudaden shiga da kundin tarukan kwamitocin karamar hukuma domin tabbatar da kashe kudaden Gwamnati ta hanyar da ta dace domin wanzuwar shugabanci nagari.

A cewar sa, daga yanzu Daraktan tsare-tsare ya zamo daga cikin masu rattaba hannu kan takardun kashe kudade, mataimakin shugaban karamar hukumar zai rike sashen kula da ruwa da tsafta a matsayin Kansila maras gafaka.

Yayi nuni da cewar, akwai bukatar karamar hukumar ta gina ajujuwa guda 2 na makarantun ‘ya’Yan fulani makiyaya domin shigo da su cikin tsare tsaren ci gaban al’umma.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Kirikasamma, Alhaji Muhammad Maji Wakili Marma, ya lura da gudummawar da bangaren majalisa ke bayarwa wajen gudanar da harkokin Gwamnati a matakin jiha da kananan hukumomi.

Alhaji Maji Wakili ya bada tabbacin aiki da shawarwari Kwamatin domin karfafa matarka cigaban karamar hukumar.

Sauran Yan Kwamatin sun hadar da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da sakataren Kwamatin Kuma Akawun Majalisa Alhaji Yusha’u Muhammad, da oditoci biyu da mataimakan sakatare.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar wakilin mazabar

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa

Manajar  ofishin na NIWA,  da ke a jihar ta Legas Injiniya Sarat Braimah ta bayyana cewa, tura ma’ikatan hukumar domin yin aikin, zai taimaka wajen gudanar da aikin a cikin inganci.

Kazalika, ya sanar da cewa, hakan zai kuma bayar da damar yin safarar kaya a cikin sauki da kuma safarar matafiya da ke bin hanyar ruwa ta yankin na Ikorodu.

“Mun yi nazari a cikin kwanciyar hankali kan yadda za a tabbatar da an cire fulawar da ke a cikin kasan ruwan ba tare da wata miskila ba tare da kuma bai wa jiragen ruwan damar yin zirga-zirgarsu a hanyoyin ruwan, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Injiya Braimah.

“ Aikin ya wuce batun fannin samar da saukin yin sufurin jiragen ruwan har da tabbatar da an kiyaye janyo matsala ga ayyukan kamun Kifi a hanyoyin na ruwan, “ A cewar Inji Manajar.

Ta kara da cewa, babban shugabanmu na hukumar ta NIWA,  Bola Oyebamiji, ne tuni ya riga ya bayar da kwangilar yin aikin, ba wai a jihar Legas kawai ba, har da a sauran hanyoyin ruwa  da ke a sassan kasar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Labarai Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala November 2, 2025 Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari