Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Kirikasamma
Published: 23rd, July 2025 GMT
Kwamatin kananan hukumomi na Majalisar Dokokin jihar Jigawa ya duba ayyukan raya kasa da karamar hukumar Kirikasamma ta samu nasarar gudanarwa daga watan Oktobar 2024 kawo yanzu.
Shugaban Kwamatin, Alhaji Aminu Zakari, ya kafa kananan kwamitoci guda biyu domin samun nasarar tantance ayyukan a cikin garin Kirikasamma da kauyuka.
Karamin Kwamati na daya bisa jagorancin wakilin mazabar
Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashimu Kanya, ya duba aikin sanya soma da tona riniyar tuka tuka a mayanka da magudanin ruwa a garin Marma da aikin gina rumfunan kasuwa a garuruwan Tasheguwa, Marma, Dilmari da Madaci.
Alhaji Ibrahim Hashim Kanya ya bayyana wa shugaban kamsilolin karamar hukumar wanda ke yiwa tawagar rakiya, Malam Isyaku Abdullahi, muhimmancin ziyarar duba ayyukan Gwamnati dan tabbatar da inganci.
Sai Kuma karamin Kwamati na biyu bisa jagorancin wakilin mazabar Kiyawa Alhaji Yahaya Muhammad Andaza wanda ya duba aikin gyaran hanyar Gafta zuwa Baturiya akan fiye da naira milyan 4 da dubu dari 2, wadda ambaliyar ruwa ta lalata a daminar bara da kuma aikin gina rumfar kasuwa a garin Baturiya.
Tun da farko a sakatariyar karamar hukumar Kirikasamma, Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa Kuma wakilin mazabar Gwiwa,
Alhaji Aminu Zakari ya ce ziyarar Kwamatin na daga nauyin da tsarin mulki ya dorawa bangaren majalisa wajen duba manufofi da shiryeyen Gwamnati baya da yin doka da amincewa da kasafin kudin kowacce shekara.
Alhaji Aminu Zakari ya ce Kwamatin Yana duba kundin bayanan harkokin Kudi da na sha’anin Mulki da su ka hadar da littafin shiga da fitar kudade da takardun biyan kudade na voucher da alkaluman tattara kudaden shiga da kundin tarukan kwamitocin karamar hukuma domin tabbatar da kashe kudaden Gwamnati ta hanyar da ta dace domin wanzuwar shugabanci nagari.
A cewar sa, daga yanzu Daraktan tsare-tsare ya zamo daga cikin masu rattaba hannu kan takardun kashe kudade, mataimakin shugaban karamar hukumar zai rike sashen kula da ruwa da tsafta a matsayin Kansila maras gafaka.
Yayi nuni da cewar, akwai bukatar karamar hukumar ta gina ajujuwa guda 2 na makarantun ‘ya’Yan fulani makiyaya domin shigo da su cikin tsare tsaren ci gaban al’umma.
A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Kirikasamma, Alhaji Muhammad Maji Wakili Marma, ya lura da gudummawar da bangaren majalisa ke bayarwa wajen gudanar da harkokin Gwamnati a matakin jiha da kananan hukumomi.
Alhaji Maji Wakili ya bada tabbacin aiki da shawarwari Kwamatin domin karfafa matarka cigaban karamar hukumar.
Sauran Yan Kwamatin sun hadar da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da sakataren Kwamatin Kuma Akawun Majalisa Alhaji Yusha’u Muhammad, da oditoci biyu da mataimakan sakatare.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar wakilin mazabar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
A wani gagarumin mataki na karfafa yaki da rashin tsaro, gwamnatin jihar Zamfara ta gudanar da wani babban taron masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a Gusau, da nufin karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomi da kuma kaddamar da sabbin dabarun yaki da ayyukan ta’addanci da masu aikata laifuka.
Taron wanda aka gudanar a Sakatariyar JB Yakubu wanda ofishin sakataren gwamnatin jihar (SSG) ya shirya, ya hada manyan hafsoshin tsaro, manyan jami’an gwamnati, da wakilan hukumomin tarayya domin duba halin tsaro da jihar ke ciki.
A cewar wata sanarwa da babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga SSG, Suleman Ahmad Tudu, ya yi, an kira taron ne domin zurfafa hadin kai a tsakanin masu ruwa da tsaki domin kara inganta ayyukan da ake gudanarwa a fadin jihar.
Sakataren gwamnatin jihar, Malam Abubakar Nakwada, wanda ya jagoranci taron, daga bisani mataimakin gwamnan jihar, Mani Malam Mummuni, ya jadadda kudirin gwamnatin jihar na siyasa na maido da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.
A cewar sanarwar, yayin taron, mahalarta taron sun tsunduma cikin wani muhimmin nazari kan kalubalen tsaro da ake fama da su tare da daukar sabbin shawarwari guda goma da gwamnatin jihar ta bullo da su.
Ta ce an tsara matakan ne don karfafa nasarorin da aka samu a baya-bayan nan da kuma kara kaimi wajen yaki da ‘yan fashi.
Da yake jawabi, Malam Nakwada ya yabawa jajircewa da sadaukarwar jami’an tsaro da ke aiki a fadin jihar Zamfara.
“Gwamnatin Jiha ta yaba da irin sadaukarwar da ku da manyan jami’an ku suka yi wajen kare lafiyar al’ummarmu, a madadin Mai Girma Gwamna Dauda Lawal, ina mika godiyarmu ga sadaukarwar da kuke yi ba tare da gajiyawa ba.” Inji shi.
SSG ya jaddada bukatar daidaitawa da dabarun hadin gwiwa wajen tinkarar barazanar da ke tasowa, inda ya bayyana cewa, hazaka, kirkire-kirkire, da hadin kai na ci gaba da zama muhimmi wajen samun zaman lafiya mai dorewa.
Ya kara da cewa, “domin tunkarar kalubalen tsaro masu sarkakiya yadda ya kamata, dole ne mu ci gaba da daidaitawa, yin sabbin abubuwa, da kuma yin aiki tare ba tare da wata matsala ba fiye da kowane lokaci.
Malam Nakwada ya kuma bayyana bakin cikinsa kan yawaitar hare-hare a sassan jihar, inda ya mika sakon ta’aziyyar gwamnati ga iyalai da al’ummomin da abin ya shafa.
“A madadin gwamnatin jihar Zamfara, ina jajantawa duk wadanda hare-haren baya-bayan nan ya rutsa da su, ina kuma tabbatar wa ‘yan kasa cewa ba za mu yi kasa a gwiwa ba har sai an samar da cikakken zaman lafiya a tsakanin kowace al’umma,” inji shi.
Ya kuma kara nanata kudirin Gwamna Dauda Lawal na samar wa jami’an tsaro kayan aiki, da tallafin da ake bukata domin fatattakar masu aikata miyagun laifuka da ke barazana ga zaman lafiya da tsaro a jihar Zamfara.
A nasa jawabin rufe taron mataimakin gwamna Mani Malam Mummuni ya yaba da gudunmawar da masu ruwa da tsaki suka bayar tare da yin kira da a kara himma da hadin kai.
“Muna matukar godiya da kokarin da aka yi ya zuwa yanzu, amma dole ne mu kara himma. Bari mu tabbatar da kowane inci na jihar mu da muke so mu maido da fata ga jama’armu,” in ji shi.
Taron dai wani mataki ne mai jajircewa da gwamnatin Dauda Lawal ta dauka na magance matsalolin tsaro a gaba, yayin da gwamnatin ke kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Zamfara.
REL/AMINU DALHATU