A wani roko da wata kungiya da aka fi sani da Sokoto Heritage Reloaded Initiative ta yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya cika alkawarin da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dauka a lokacin wata ziyarar aiki da ya kai a jihar.

 

An yi wannan roko ne a yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a jihar Sokoto, inda shugaban kungiyar Farfesa Uthman Abdulqadir, ya jaddada muhimmancin girmama abubuwan da Shagari ya bari.

 

Ya tuna cewa shugaba Buhari ya yi wannan alkawari ne a ziyarar da ya kai Sokoto.

 

Farfesa Uthman ya bayyana irin rawar da Shehu Shagari yake takawa wajen ciyar da ilimi gaba a Najeriya, inda ya bayyana cewa ya taka rawa wajen aza harsashin kafa Budaddiyar Jami’ar Nijeriya.

 

Ya bayyana Shagari ba wai kawai shugaba ba, a’a a matsayin alama ce ta tawali’u, rikon amana da kishin kasa, mutumin da ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa kasarsa hidima.

 

Farfesa Uthman ya bayyana kwarin guiwar cewa shugaba Tinubu, wanda ya shahara da mutunta shuwagabannin kasa da jajircewar hadin kai, zai gane muhimmancin tunawa Shehu Shagari.

 

Ya yi imanin cewa wannan aikin zai bayyana a fili karara Tinubu a matsayin jagora mai girmama kimar tawali’u, hidima, da kishin kasa.

 

Farfesa Uthman ya jaddada cewa sanyawa wurare sunayen Dattijai ba karamin alfanu ne ga rayuwa jama’ar ba.

 

Ya bayyana shi a matsayin muhimmin kayan aiki don ilimi, zaburarwa, da kuma kiyaye dabi’un da suka dace da al’ummomin yanzu da na gaba.

 

NASIR MALAL

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Shagari Farfesa Uthman

এছাড়াও পড়ুন:

Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21

Yuro biliyan 4

Yen biliyan 15 (na Japan)

Tallafin dala miliyan 65

Kuma aron cikin gida ta hanyar sayar da hannun jarin gwamnati (bond) na kusan Naira biliyan 757.

Har ila yau, akwai shirin tara kuɗi har dala biliyan 2 ta hanyar takardun lamuni da za a fitar cikin ƙasa amma a kuɗin ƙetare.

Shugaban kwamitin kasafi, Sanata Olamilekan Solomon, ya ce wannan amincewa tsarin doka ce kawai, domin an riga an haɗa bashin cikin tsare-tsaren kasafin kuɗi da MTEF tun da farko.

Sanata Sani Musa (Niger Ta Gabas) ya bayyana cewa wannan shiri ba na shekara ɗaya ba ne, amma zai shafi rabon kuɗi na tsawon shekara shida, yana mai jaddada cewa Nijeriya ba ta taɓa gazawa wajen biyan bashinta ba.

Shugaban kwamitin Bankuna da harkokin kuɗi, Sanata Adetokunbo Abiru (Lagos Ta Gabas), ya tabbatar da cewa dukkan bashin na bin ƙa’idojin dokar kula da bashi da ta ɗabi’un da suka dace da dokar kuɗi.

Sai dai Sanata Abdul Ningi (Bauchi Ta Tsakiya) ya nuna damuwa game da ƙarancin bayani da ake da shi kan yadda za a raba bashin da kuma hanyoyin da za a biya su.

Ya nemi a bayyana adadin da kowace jiha ko hukuma za ta samu, da kuma amfanin bashin domin a iya bayyana wa al’umma gaskiya.

A cikin jerin ayyukan da za a aiwatar da kuɗin akwai:

Gina layin dogo daga Fatakwal zuwa Maiduguri

Tsarin wutar lantarki da sadarwa na zamani

Harkokin tsaro

Noma da aikin gidaje

Sanata Victor Umeh (Anambra Ta Tsakiya) ya goyi bayan shirin, yana mai bayyana cewa wannan ne karon farko da ake ware dala biliyan 3 domin gina layin dogo a gabashin Nijeriya.

Mataimakin Shugaban Majalisa, Barau Jibrin ya yabawa kwamitin bisa aikin da ya yi, yana mai cewa “dukkan yankunan ƙasa na cikin shirin kuma hakan na nuna cewa Agenda ta ‘Renewed Hope’ tana aiki.”

Majalisar ta jaddada cewa duk wani kuɗin da za a fitar dole ne a yi amfani da shi ne kawai wajen ayyukan raya ƙasa da ci gaban al’umma, bisa tanadin dokar kuɗin gwamnati.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare
  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  • Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
  • Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Tsoffin Jami’an ‘Yan Sanda Sun Bukaci A fitar Da Su Daga Cikin Shirin Fansho
  • Gwamna Namadi Ya Jinjinawa Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Bisa Ayyukan Raya Kasa
  • APC Ta Zabi Kamilu Sa’idu A Matsayin Dan Takarar Kaura Namoda Ta Kudu A Zamfara
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne