Babbar Kotun Tarayya da ke Bauchi ta yanke hukunci a kan gwamnatin jihar Bauchi da ta biya tsohon Akanta-Janar na jihar, Dakta Sa’idu Abubakar, Naira miliyan 100 a matsayin diyyar take masa haƙƙi da kuma tsare shi ba bisa ƙa’ida ba. Kotun ta kuma umarci gwamnati ta wallafa ban haƙuri a manyan jaridu guda biyu cikin kwanaki 14.

Mai Shari’a Aminu Garba ya yanke wannan hukunci ne a ƙarar da Dakta Abubakar ya shigar, yana zargin gwamnati da jami’anta da take masa haƙƙi, da kama shi ba tare da bin ƙa’ida ba, da musgunawa. Ya bayyana cewa hakan ya saɓawa tanade-tanaden kundin tsarin mulki da kuma yarjejeniyar kare haƙƙin bil’adama ta Afrika.

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

Waɗanda kotun ta bayyana da laifi sun haɗa da shugaban ƴansanda na ƙasa, kwamishinan ƴansanda na Bauchi, gwamnatin jihar Bauchi, Antoni Janar na jihar da hukumar karɓar ƙorafe-ƙorafe ta jihar. Kotun ta tsame hukumar DSS daga cikin hukuncin, saboda babu isasshen hujja kan rawar da ta taka.

A ƙarshe, kotun ta hana duk wani ƙarin cin mutunci, tsarewa ko kama Dakta Abubakar ba tare da bin doka ba. Haka kuma ta jaddada cewa ya cancanci diyya saboda hana shi walwala da damuwa da aka jefa shi ciki daga ranar 9 zuwa 25 ga Disamba, 2024.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.

 

“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar