HausaTv:
2025-07-11@22:29:30 GMT

HKI Ta Roki Amurka Ta Taimake Ta A Fada Da Kasar Yemen

Published: 11th, July 2025 GMT

Tashar talabijin din “Cane” ta HKI ta bukaci Amurka da ta kafa kawance mai fadi na kasashe domin fuskantar kasar Yemen.

A yayin ziyarar da Fira ministan HKI, Benjamin Netanyahu a Amurka ne dai ya bijiro da wannan bukatar, kamar yadda rahoton tashar talabijin din ta “Cane” ya ambata.

 Rahoton ya kuma ce, Jami’an HKI sun sanar da Amurka cewa, ci gaba da hare-haren Yemen, ya tashi daga zama matsalarta ita kadai, don haka da akwai bukatar kai hare-hare na hadin gwiwa da Amurka da kuma shigar da kasashen wannan yankin da kuma wasu na duniya.

Tun daga 2023 ne sojojin Yemen suke kai wa jiragen ruwa na HKI hare-hare a cikin tekun “Red Sea” ko kuma wadanda su ka nufi tasoshinta na jirgin ruwa. Sojojin na Yemen dai sun sha bayyana cewa ba za su daina kai hare-haren ba har sai an kawo karshen yakin Gaza, da kuma dauke takunkuman da aka kakabawa yankin.

Shugaban kungiyar Ansarullah ta Yemen Sayyid Abdulmalik al-Husi ya sha bayyana matsayar kasar ta Yemen yana mai cewa; Hare-haren nasu martani ne akan laifukan yakin da HKI take  yi a  Gaza, ba kuma za su daina ba, sai an dakatar da aikata wadannan laifukan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Zagaye na 5 A Tattaunawar Gaza da HKI  Ya tashi ba tare da Sun Dai-daita ba A Doha

Tattaunawa na baya-bayan nan tsakakin HKI da Hamas ya tashi ba tare da wani ci gaba ba a birnin Doha na kasar Qatar. Idan an cimma wannan yarjeniyar dai ana saran musayan fursinoni 10 na HKI sannan za’a saki wasu da dama dake hannun HKI,

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa rashin nasarar wannan taron ya sanya makomar yaki a Gaza cikin rudu don yanzun kuma ba’a san abinda zai faru ba. Kuma bamu san manufar HKI ba a wannan yakin.

Wani jami’in Falasdinawa ya fadawa tashar talabijin ta Al-Sharq kan cewa da alamun tawagar yahudawan sunzo ba taren da niyyar cimma wani Abu ba, tunda duk abunda aka  tambayesu sai suce sai sun tambayi tel-Aviv, wanda ya nuna basu zo don cimma wata yarjeniya ba.

Don haka jami’in ya zargi HKI da wargaza tattaunawar. Mai yuwa kuma suna kan shirin na korar Falasdinawa daga Gaza gaba daya,

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanonin Jiragen Ruwa Sun Yanke Hulda Da Isra’ila Saboda Matsalar Hare-Haren Kasar Yemen
  • Qalibof: Asarorin HKI A Yakin Kwanaki 12 Yafi Abinda Ta Bayyana
  • Mayakan Huthi Sun Kara Kai Wasu Hare-Hare da Makamai Masu Linzami Kan BenGurio
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci  ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Zagaye na 5 A Tattaunawar Gaza da HKI  Ya tashi ba tare da Sun Dai-daita ba A Doha
  • Abdullahi Ojlan Ya Sanar Da Kawo Karshen Fada Da Makami
  • Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Amince Iran ta Kai Hare-Hare Kan cibiyoyin Sojojinta Guda Biyar
  • Hizbullah Ta Kasar Lebanon Ta Godewa JMI Dangane Da Tallafawa Kungiyar Saboda Gwagwarmaya Da HKI