Aminiya:
2025-07-31@12:36:27 GMT

Aminu Bayero ya soke hawan Sallah

Published: 27th, March 2025 GMT

Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya sanar da soke bukukuwan Sallah na bana, saboda bukatar tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar.

A wata sanarwa da aka fitar, Sarkin ya bayyana takaicinsa kan matakin amma ya jaddada cewa, tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi shi ne babban abin da ya sa a gaba.

Sarkin ya ce, “Bisa umarnin da jama’a suka ba mu da kuma jajircewar da muka yi na ba su kariya, mun ga ya dace mu janye duk wani shiri da aka yi na bukukuwan Sallah bisa la’akari da halin da ake ciki.”

Ya kara da cewa, tuntubar da aka yi da manyan malaman addini da sauran masu ruwa da tsaki sun yi tasiri a kan shawarar.

Ya kuma jaddada cewa, duk da cewa bikin Sallah al’ada ce mai kima, bai kamata ta zo da rashin zaman lafiya da kwanciyar hankali ba.

Name(required) Email(required) Website Message

Submit

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aminu Ado Bayero Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta taya sabon mai martaba Sarkin Katsinar Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, murnar hawansa karagar mulki a matsayin Sarkin Katsinan Gusau na 16.

 

Jam’iyyar a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren yada labaranta, Yusuf Idris Gusau, ta bayyana sabon sarkin a matsayin mai tarihi da kuma nadin sarautar Allah, wanda ya zo ne jim kadan bayan rasuwar mahaifinsa, marigayi sarki, Alhaji Ibrahim Bello.

 

Sanarwar ta nuna cewa Alhaji Abdulkadir kyawawan halaye na gaskiya, kwazonsa, sadaukarwa, biyayya ga mahaifinsa da ya rasu, da kuma mutunta al’umma ta kowane hali, sun nuna shi ne wanda ya cancanta.

 

A cewar sanarwar, wannan shi ne karo na farko a tarihin masarautar da wani dan da ya haifa kai tsaye ya gaji mahaifinsa, wanda jam’iyyar ta ce hakan yana nuna yardar Allah da kuma ci gaba da gadon adalci na marigayi sarki.

 

Jam’iyyar APC ta bukaci sabon sarkin da ya kiyaye dabi’u da abubuwan gado na mahaifinsa da kakanni, musamman na fitaccen malamin addinin musulunci kuma shugaba, Sambo Dan-Ashafa.

 

Jam’iyyar ta yi addu’ar Allah ya yi masa jagora, ya kare shi, da kuma hikimar Sarki don ya jagoranci al’umma zuwa ga zaman lafiya da wadata.

 

Har ila yau, ta ba da tabbacin ci gaba da goyon bayanta da shirye-shiryenta na neman shawara, jagoranci, da albarka daga sabon sarki.

 

Daga karshe sanarwar da sakon fatan alheri ga mai martaba sarki da daukacin masarautar Gusau.

 

 

REL/AMINU DALHATU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
  • Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16
  • Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza