NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe
Published: 23rd, July 2025 GMT
Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC), tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Jihar Yobe, sun fara rabon kayayyakin gini ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a ƙananan hukumomi 13 na jihar.
Wannan taimako na da nufin tallafa wa mutanen da ambaliya ta rushe musu gidaje.
Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule Lamido An kone babur din ‘barayin waya’ a KanoA lokacin da aka fara rabon kayayyakin a Damaturu, wakilin babban daraktan NEDC, Farfesa Ibrahim Ali Abbas, ya ce hukumar ta kawo kayayyakin rufin gida da sauran kayan gini don taimaka wa mutane su gyara ko sake gina gidajensu.
Baya ga wannan, hukumar ta kuma bai wa Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA), kayan aikin ceto, domin su kasance cikin shiri idan wani iftila’i ya sake faruwa a wannan daminar.
Babban jami’in na NEDC ya roƙi shugabanni da su raba kayan cikin gaskiya da adalci, kuma a tabbatar cewa kayan sun kai hannun masu buƙata yadda ya dace.
A nata ɓangaren, Kwamishiniyar Ma’aikatar Agaji da Jin-ƙai ta Jihar Yobe, Dokta Mairo Ahmed Amshi, ta yaba wa hukumar NEDC saboda taimakon a kan lokaci.
Ta ce wannan matakin zai rage wa mutanen da ambaliya ta shafa raɗaɗi da damuwa.
Ta kuma tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa waɗanda abin ya shafa, da kayan abinci, magunguna da kuma sansanin zama na wucin gadi.
Amma ta buƙaci shugabannin al’umma da su kula da yadda ake raba kayan, sannan ta roƙi wadanda suka samu tallafin da su yi amfani da shi wajen gina gidajen da za su ba su kariya da kwanciyar hankali.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kayan Gini
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
Hukumar Tace Fina-Finai da Dab’i ta Jihar Kano ta haramta shirya duk wata muƙabala tsakanin mawaƙan yabon Annabi (S.A.W), tare da gayyatar mawaƙa Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi su bayyana a gabanta.
Hukumar ta kuma gayyaci mawaƙan ne tare da sauran waɗanda suka jagoranci muƙabalar da fitattun mawaƙan biyu suka yi ranar Litinin, da su bayyana a gabanta cikin sa’o’i 24.
Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin TinubuHakan na zuwa ne ƙasa da kwana ɗaya bayan ɓullar wata muhawara da aka yi tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi kuma ta karade shafukan sada zumunta, wacce hukumar ta bayyana a matsayin karya dokokin aikinta.
Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da hakan ranar Talata, inda ya ce ɗaukar matakin wani yunƙuri ne na tabbatar da zaman lafiya, daidaito da bin doka tsakanin mawaƙan nishaɗi da na addini.
El-Mustapha, a cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, ya kuma ce an haramta duk wata nau’in muƙabala daga mawaƙan addini a jihar ba tare da izinin hukumar ba.
A yayin da yake ƙaddamar da wani kwamitin bincike da shugaban hukumar ya naɗa karkashin Daraktan Ayyuka na Musamman a hukumar, Isah Abdullahi, El-Mustapha ya umarci waɗanda aka gayyatar da su bayyana a gaban kwamitin domin amsa tambayoyi.
Hukumar ta ce shirya irin waɗannan muhawara ba tare da izininta ba ya saɓa doka kuma zai iya jawo hukunci mai tsanani ga wanda suka karya.
Hukumar ta kuma jaddada ƙudirinta na ci gaba da kula da ayyukan mawaƙan da masu nishaɗantarwa a faɗin jihar tare da yin kira ga jama’a da su zauna lafiya sannan su ci gaba da ba ta haɗin kai a ayyukanta.