Wata Kungiyar Kare Hakkin Bil’adama Ta Bukaci A Hukunta Trump Kan Rabon abinci Ko Tarkon Mutawa A Gaza
Published: 13th, July 2025 GMT
Kungiyar kare hakkin bil-adama ta – The Euro-Mediterranean Human Rights Monitor ta bukaci a hukunta gwamnatocin Amurka da HKI kan shirin rabon abincin da suke gudanarwa a gaza, wanda ya kai ga mutuwar Falasdinawa da dama.
Kungiyar ta bayyana cewa kasashen biyu sun hada kai don fiyar da falasdinawa wadanda suke fama da yunwa a cikin gaba, a inda sojoji HKI zata kashe su.
Rahoton ya kara da cewa, misali guda shi ne abinda ya faru a yankin Ash-shakoush inda sojoijin HKI suka kashe falasdinawa akalla 30 wadanda suka fito don karban abinci. Sannan suka raunata wasu 180.
HKI tare da Amurka sun hana abinci shiga Gaza ta kofar Rafah da kuma Kerin Abu saleh na tsawon watanni, har sai da Falasdinawa bas u da zabi ko sum utu yunwa ko kuma su fito karban abinci inda sojojin yahudawan zasu samesu su kashe su a kan abincin da ba zasu ci ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Columbia Ya Yi Dirar Mikiya Kan Donald Trump Kan Bai Wa Isra’ila Makamai
Shugaban Kasar Columbia Ya Soki Donald Trump Akan Bai Wa Isra’ila Makamai
Shugaban na kasar Columbia Gustavo Petro ya ce, Bugun kirjin da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi na bai wa “Isra’ila” makamai tare da cewa ta yi amfani da su da kyau, ba wani abu ne da ya cancanci a yi masa tafi, sunan shi tarayya a aikata laifi.
Shugaba Gustavo Petro yana mayar da martani ne akan zancen da shugaban kasar Amurka ya yi a Majalisar “Knesset’ ta Haramtacciyar Kasar Isra’ila ya ce; Isra’ilan ta yi amfani da makaman da ya ba ta da kyau.
Shugaba Gustavo ya kara da cewa; wadannan makaman na Amurka sun kashe mutane 70,000 sannan kuma sun jikkata wasu 200,000.
Shi dai shugaban kasar ta Columbia yana daga cikin na gaba-gaba wajen sukar lamirin Haramtacciyar Kasar Isra’ila saboda yakin Gaza da kuma Amurka wacce take goya mata baya.
A lokacin taron babban zauren Majalisar Dinkin Duniya na karshen nan, shugaba Gustavo Petro ya shiga cikin masu Zanga-zanga a birnin Newyork domin nuna goyon bayan Gaza da kuma yin kira da a kawo karshen yaki. Haka nan kuma kasarsa ta yanke huldar diplomasiyya da Haramtacciyar Kasar Isra’ila.
A wani jawabinsa na bayan fagen taron na Majalisar Dinkin Duniya, ya yi kira da a kafa rundunar kasa da kasa domin ‘yanto da Falasdinu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Jihadul-Islami Ta Falasdinu Ta Ce; ‘Yantar Da Fursunonin Falasdinawa Abu Ne Mai Muhaimmanci October 15, 2025 Majalisar Dinkin Duniya Ta Bayyana Cewa: Sake Gina Gaza Zai Ci Dala Biliyan 70 October 15, 2025 Araghchi : Trump bai cancanci mai samar da zaman lafiya ba October 14, 2025 UNDP : An ruguza fiye da kashi 80 cikin 100 na gine-ginen Gaza October 14, 2025 Sojojin Madagaska sun karbe mulkin kasar October 14, 2025 Trump ya ce zai yi shawara game da batun kafa kasar Falasdinu October 14, 2025 Islamic Jihad : jarumtakar ‘yan gwagwarmaya ce ta haifar da sako fursunonin falasdinawa October 14, 2025 Aragchi Yana Uganda Don Halattan Taron Ministocin Kungiyar NAM October 14, 2025 Iran Ta Jadda Cewa A Shirye Take Ta Kare Kanta A Duk Wani Yaki Wanda Makiya Zasu Dora Mata October 14, 2025 Ma’aikatar Harkokin wajen Kasar Iran Ta Yi Tir Da Jawabin Trump A Knesset Ta HKI October 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci