HKI Ta Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Kan Kudancin Kasar Lebanon
Published: 11th, July 2025 GMT
A dai-dai lokacinda jiragen yakin HKI suke ci gaba da kai hare-hare kan mutanen kudancin Lebanon sannan suka ci gaba da keta hurumin yarjeniyar da aka cimma da kungiyar Hizbullah, tana kashe mutanen kasar Lebanon. A wani bangare kuma Sojojin UNIFEL suna fuskantar turjiya daga mutanen kudancin kasar ta Lebanon.
Jaridar Arba News ta kasar Saudia ta bayyana cewa mutane a yankin sun hana sojojin UNIFEL shiga wasu unguwanni a yankin don gudanar da bincike a cikin gidajen mutane.
Labaran da suke fitowa daga irin wadannan yankuna sun nuna cewa muatne sun hana sojojin nUnufel shiga wasu unguwanni, sai sun kawo sojojin kasar Lebanon .
Sojojin sun dage saisun shiga amma mutane sun hansu shiga a sannane suka fara amfani da teas gas ko iska mai sa hawaye don tarwatsa su. Wannan bai yi amfani ba.
Gwamnatin kasar Lebanon ta bukaci a tsawaita lokacin wanzuwar sojojin UNIFEL a kudancin Lebanon amma ta bayyana a fili sojojin suna aiki wa HKI da Amurka ne.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinawa 13 Ne Suka Yi Shahada Wasu Da Dama Suka Jikkata A Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila A Gaza
Falasdinawa 13 ne suka yi shahada da suka hada da yara kanana da mata a hare-haren bama-bamai da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan gidaje da matsugunan Falasdinawa a Gaza
Sojojin mamayar Isra’ila sun ci gaba da kai hare-hare a zirin Gaza da asubahin ranar Talata, inda suka kai hare-hare kan gidajen fararen hula da matsugunan ‘yan gudun hijira. Hare-haren sun yi sanadiyyar shahadan fararen hula 13 da suka hada da yara da mata, yayin da wasu da dama suka jikkata a wasu munanan hare-hare ta sama da aka kai a yankuna daban-daban na zirin.
Asibitin Al-Shifa ya sanar da shahadan Falasdinawa hudu ciki har da wani jariri, sakamakon harin da jiragen yakin sojin mamayar Isra’ila suka kai a wani gida da ke kusa da kasuwar Carrefour a unguwar Tel al-Hawa da ke kudu maso yammacin birnin Gaza. A halin da ake ciki kuma, asibitin Baptist ya sanar da shahadan Falasdinawa biyu tare da jikkata wasu sakamakon harin da aka kai a gidan Khader al-Jamasi da ke kusa da masallacin al-Ibki da ke unguwar al-Tuffah da ke gabashin birnin.
Wata majiyar lafiya a asibitin Al-Awda da ke sansanin ‘yan gudun hijira na Nuseirat ta bayyana cewa: Hari ya jikkata wasu fararen hula a lokacin da makarantar Abu Helu al-Sharqiya da ke dauke da ‘yan gudun hijira a sansanin ‘yan gudun hijira na al-Bureij da ke tsakiyar zirin Gaza ta fuskanci hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila ta kai kai tsaye, lamarin da ya haifar da firgici ga iyalan da suka rasa muhallansu.