Aminiya:
2025-11-02@20:54:35 GMT

Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa

Published: 23rd, July 2025 GMT

Dakatacciyar Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta lashi takobin sake maka shugabancin Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio a gaban kotun daukaka kara bayan an hana ta shiga harabar majalisar a ranar Talata.

Cikin bacin rai, Natasha ta shaida wa ’yan jarida cewa za ta tattauna da lauyoyinta cikin gaggawa domin fara shigar da karar, tana mai cewa matakin ya saba da hukuncin kotun da ta bayar da umarnin a mayar da ita kan kujerarta.

Lamarin dai ya biyo bayan yadda jami’an tsaron da ke gadin majalisar suka tare hanya suka hana tawagar motocinta shiga majalisar, duk kuwa da umarnin kotu na mayar da ita.

HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare

Ta kuma ce hatta dakatar da itan ma da farko ba ya kan ka’ida.

A cewar ta, “Yanzu zan je na tattauna da lauyoyina domin shirin daukaka kara alabasshi kotu ta fassara mana abin da ya faru. Ni mace ce mai bin dokokin kasa.”

Sanatar ta kuma yi alla-wadai da matakin da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio ya dauka na hana ta shigar, inda ta ce hakan tamkar raina kotu ne.

Ta kuma ce, “Akpabio bai fi karfin kundin tsarin mulkin Najeriya ba. Ina so ’yan Najeriya su sani cewa ba Ofishin Shugaban Majalisar Dattawa ne ya mayar da ni Sanata ba.

“Duk da cewa ya tafi daukaka kara, hakan ba yana nufin cewa ya soke hukuncin Mai Shari’a Binta Nyako ba ne kuma hakan ba zai dakatar da ni daga kasancewa Sanata ba.

“Mutanen Kogi ta Tsakiya ne suka zabe ni kuma su nake wakilta,” in ji Natasha.

Tun da farko dai Sanatar ta yi yunkurin shiga majalisar tare da magoya bayanta amma, amma aka hanata, dole sai da ta sauka ta tafi a kafa.

An dai girke tarin jami’an tsaron da ba a saba ganin irin su ba a majalisar, inda aka ga wasu jami’an na duba motoci tare da ma takaita yawan wadanda za su ajiya ababen hawa a wajen fakin na wajen majalisar.

Akalla an ga motocin sintiri na jami’an ’yan sanda guda biyar da aka girke a muhimman wuraren shiga majalisar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: a majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

 

Yayin ganawarsa da firaministan Thailand, Shugaba Xi Jinping ya ce a shirye kasarsa take ta karfafa hadin gwiwa da Thailand kan dabarun samun ci gaba, tare kuma da gabatar da gogewarta na samun ci gaba a sabon zamani, kuma ya yi kira da a gaggauta gina layin dogo tsakanin Sin da Thailand da bunkasa hadin gwiwa a bangaren cinikin amfanin gona da tattalin arziki mai kiyaye muhalli da kuma kirkire kirkiren fasaha. (Mai fassara: FMM)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa