Aminiya:
2025-09-17@23:19:50 GMT

Kotu ta aike mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato

Published: 11th, July 2025 GMT

Wata Kotu a Jos, Babban Birnin Jihar Filato, ta tura mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Jihar Filato zuwa gidan yari.

Ana zarginsu da kashe wasu ’yan ɗaurin aure a ƙauyen Mangun da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a jihar.

Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki

Mutanen da aka kashe suna cikin wata motar haya da ta taso daga Basawa a Karamar Hukumar Sabon Gari ta Jihar Kaduna.

Baƙin suna kan hanyarsu ta zuwa ƙauyen Kwa a Ƙaramar Hukumar Qua’an Pan da ke Jihar Filato domin halartar ɗaurin aure.

Wasu ɓata-gari ne suka kai musu hari.

Ɓata-garin sun kashe mutum 13, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Mata, maza da yara na cikin motar wadda ke ɗauke da fasinjoji 32.

A ranar Alhamis, ‘yan sanda suka gurfanar da mutum 22 a kotu bisa zargin kashe baƙin.

Amma kotu ba ta bayyana matsayinta ba saboda lauyan da ke kare waɗanda ake zargin, Garba Pwul, ya ce akwai yara ƙanana guda biyu a cikinsu ɗaya yana da shekaru 13, ɗaya kuma shekaru 17 kuma bai kamata a gurfanar da su ba.

Alƙalin kotun ya amince da hakan kuma ya umarci ’yan sanda su cire su daga cikin jerin waɗanda aka gurfanar.

An sake gurfanar da mutum 20

A ranar Juma’a, ’yan sanda suka sake gurfanar da sauran mutum 20.

Ana tuhumar su da laifuka guda hudu: haɗa kai wajen aikata laifi, jikkata mutane, kisa, da ƙone gawarwakin mutum 13 a ranar 20 ga watan Yuni, 2025.

’Yan sanda sun ce waɗanda ake zargin sun yi amfani da makamai masu hatsari kamar bindiga, adda, takobi da man fetur.

Dukkanin mutum 20 da ake tuhuma sun ce ba su da laifi.

Bayan sun bayyana matsayinsu, lauyan ’yan sanda ya roƙi kotu da ta tura su gidan yari tare da ɗage shari’ar zuwa wani lokaci.

Lauyan da ke kare su ya nemi a ba da belinsu, amma lauyan gwamnati ya ce bai da isasshen lokaci don ya amsa wannan buƙata bisa doka.

Alkalin kotun, Mai shari’a Boniface Ngyong, ya ce ba za a saurari buƙatar belin a yanzu ba, saboda ƙorafin da lauyan gwamnati ya gabatar.

Ya ɗage shari’ar zuwa ranar 13 ga watan Agusta, 2025, sannan ya umarci a ci gaba da tsare su a gidan yari na Jos.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure yan sanda su ɗaurin aure gurfanar da

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

Majalisar dattawa ta dakatar da Sanata Akpoti-Uduaghan a ranar 6 ga Maris, 2025, na tsawon watanni shida. Duk da cewa an kalubalanci lamarin a kotu, amma babbar kotun tarayya ba ta bayar da wani umarni na soke dakatarwar ba ko kuma tilasta sake dawo da ita bakin aiki.

 

A ranar 4 ga Satumba, 2025, Sanatar ta sanar da ofishin magatakarda akan aniyar ta na ci gaba da ayyukan majalisa, nan take, ofishin ya mika wasikar ga shugabannin majalisar dattawan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000