Kotu ta aike mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
Published: 11th, July 2025 GMT
Wata Kotu a Jos, Babban Birnin Jihar Filato, ta tura mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Jihar Filato zuwa gidan yari.
Ana zarginsu da kashe wasu ’yan ɗaurin aure a ƙauyen Mangun da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a jihar.
Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman ArzikiMutanen da aka kashe suna cikin wata motar haya da ta taso daga Basawa a Karamar Hukumar Sabon Gari ta Jihar Kaduna.
Baƙin suna kan hanyarsu ta zuwa ƙauyen Kwa a Ƙaramar Hukumar Qua’an Pan da ke Jihar Filato domin halartar ɗaurin aure.
Wasu ɓata-gari ne suka kai musu hari.
Ɓata-garin sun kashe mutum 13, yayin da wasu da dama suka jikkata.
Mata, maza da yara na cikin motar wadda ke ɗauke da fasinjoji 32.
A ranar Alhamis, ‘yan sanda suka gurfanar da mutum 22 a kotu bisa zargin kashe baƙin.
Amma kotu ba ta bayyana matsayinta ba saboda lauyan da ke kare waɗanda ake zargin, Garba Pwul, ya ce akwai yara ƙanana guda biyu a cikinsu ɗaya yana da shekaru 13, ɗaya kuma shekaru 17 kuma bai kamata a gurfanar da su ba.
Alƙalin kotun ya amince da hakan kuma ya umarci ’yan sanda su cire su daga cikin jerin waɗanda aka gurfanar.
An sake gurfanar da mutum 20A ranar Juma’a, ’yan sanda suka sake gurfanar da sauran mutum 20.
Ana tuhumar su da laifuka guda hudu: haɗa kai wajen aikata laifi, jikkata mutane, kisa, da ƙone gawarwakin mutum 13 a ranar 20 ga watan Yuni, 2025.
’Yan sanda sun ce waɗanda ake zargin sun yi amfani da makamai masu hatsari kamar bindiga, adda, takobi da man fetur.
Dukkanin mutum 20 da ake tuhuma sun ce ba su da laifi.
Bayan sun bayyana matsayinsu, lauyan ’yan sanda ya roƙi kotu da ta tura su gidan yari tare da ɗage shari’ar zuwa wani lokaci.
Lauyan da ke kare su ya nemi a ba da belinsu, amma lauyan gwamnati ya ce bai da isasshen lokaci don ya amsa wannan buƙata bisa doka.
Alkalin kotun, Mai shari’a Boniface Ngyong, ya ce ba za a saurari buƙatar belin a yanzu ba, saboda ƙorafin da lauyan gwamnati ya gabatar.
Ya ɗage shari’ar zuwa ranar 13 ga watan Agusta, 2025, sannan ya umarci a ci gaba da tsare su a gidan yari na Jos.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure yan sanda su ɗaurin aure gurfanar da
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Neja
Aƙalla mutum 13 ne suka rasu, ciki har da ɗan sanda da ’yan sa-kai guda uku, a wani hari da ’yan bindiga suka kai garin Mongoro da ke Ƙaramar Hukumar Mariga, a Jihar Neja.
Harin ya faru ne da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Laraba.
Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna SoludoMazauna garin Wamba, sun ce har yanzu suna cikin fargaba saboda ‘yan bindigar ba su bar yankin ba.
A ranar 24 ga watan Yuni, maharan sun kai hari wani sansanin sojoji da ke Kwanan-Dutse, inda suka kashe sojoji 17, tare da jikkata wasu 10.
A cewar wasu mazauna garuruwan, harin na baya-bayan nan ya faru ne a ranar Talata, inda ’yan bindigar suka zo da yawa kuma ɗauke da muggan makamai inda suka yi wa jami’an tsaro da ’yan sa-kai taron dangi.
Sun raunata mutane da dama.
Wani mazaunin yankin wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya ce jami’an tsaron sun yi ƙoƙari, amma alburusansu sun ƙare a yayin artabun, wanda hakan ya sa dole suka ja da baya.
Ya ce ana buƙatar gaggauta tallafa wa ’yan sa-kai a Mongoro saboda yankin na fama da hare-hare.
Wani mazaunin kuma ya ce an kashe mutum 13, ciki har da ’yan sa-kai, sannan ’yan bindigar sun lalata turakun sadarwa, wanda hakan ya haddasa matsalar sadarwa a yankin.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Mariga, Abbas Adamu Kasuwan-Garba, ya tabbatar da harin, amma ya ce ba a tabbatar da adadin waɗanda suka rasu ba tukuna.
Ya ƙara da cewa lamarin tsaro a yankin na ƙara taɓarɓarewa saboda yawan hare-haren da ake kai wa.
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar harin, amma ya ce har yanzu babu cikakken bayani.
Saboda tsoron kai hare-haren, manoma da dama a Mariga da Rijau sun daina zuwa gonaki, wasu kuma sun koma birane domin tsira da rayukansu.
Wani mazaunin yankin Rijau, mai suna Ibrahim Ayuba, ya ce mutane da yawa sun tsere daga ƙauyuka zuwa Rijau saboda tsoron kashe-kashe da sace-sacen da ke ƙaruwa a kullum.
A wani yunƙuri na shawo kan matsalar tsaro, Etsu Nupe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jihar Neja, Alhaji Yahaya Abubakar, ya buƙaci haɗin gwiwa da sabbin dabaru domin magance matsalar.
Ya bayyana haka ne yayin da Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Adamu Abdullahi Elleman, ya kai masa ziyara a fadarsa.
Kwamishinan, ya ce manufar ziyarar ita ce ƙarfafa haɗin kai tsakanin sarakuna, al’umma da jami’an tsaro wajen yaƙi da ’yan bindiga da sauran matsalolin tsaro.
Masani ya buƙaci kafa rundunar tsaron dajiWani masani kan harkar tsaro, Auwal Bala Durumin Iya, ya buƙaci gwamnati ta bai wa ’yan sa-kai da jami’an tsaro makaman da suka fi ‘yan bindiga nagarta.
Ya kuma bayar da shawarar a kafa sabuwar rundunar tsaro domin kula da dazuka, wanda yawancin a can ake aikata laifuka.
Ya ce dole ne a horas da dakarun rundunar sosai, a ba su makamai irin su AK-47, sannan a cire siyasa wajen kula da harkar tsaro.
Ya ce idan aka daina siyasantar da harkar tsaro, aka mayar da hankali kan ƙwarewa, za a iya cimma nasara.
Ya kuma buƙaci gwamnati ta naɗa shugabanni nagari a hukumomin tsaro, tare da tallafa wa ’yan sa-kai da kuɗi da kayan aiki, inda ya yaba wa ƙoƙarinsu duk da cewa ba sa karɓar albashi.