Aminiya:
2025-11-02@03:24:59 GMT

Kotu ta aike mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato

Published: 11th, July 2025 GMT

Wata Kotu a Jos, Babban Birnin Jihar Filato, ta tura mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Jihar Filato zuwa gidan yari.

Ana zarginsu da kashe wasu ’yan ɗaurin aure a ƙauyen Mangun da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a jihar.

Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki

Mutanen da aka kashe suna cikin wata motar haya da ta taso daga Basawa a Karamar Hukumar Sabon Gari ta Jihar Kaduna.

Baƙin suna kan hanyarsu ta zuwa ƙauyen Kwa a Ƙaramar Hukumar Qua’an Pan da ke Jihar Filato domin halartar ɗaurin aure.

Wasu ɓata-gari ne suka kai musu hari.

Ɓata-garin sun kashe mutum 13, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Mata, maza da yara na cikin motar wadda ke ɗauke da fasinjoji 32.

A ranar Alhamis, ‘yan sanda suka gurfanar da mutum 22 a kotu bisa zargin kashe baƙin.

Amma kotu ba ta bayyana matsayinta ba saboda lauyan da ke kare waɗanda ake zargin, Garba Pwul, ya ce akwai yara ƙanana guda biyu a cikinsu ɗaya yana da shekaru 13, ɗaya kuma shekaru 17 kuma bai kamata a gurfanar da su ba.

Alƙalin kotun ya amince da hakan kuma ya umarci ’yan sanda su cire su daga cikin jerin waɗanda aka gurfanar.

An sake gurfanar da mutum 20

A ranar Juma’a, ’yan sanda suka sake gurfanar da sauran mutum 20.

Ana tuhumar su da laifuka guda hudu: haɗa kai wajen aikata laifi, jikkata mutane, kisa, da ƙone gawarwakin mutum 13 a ranar 20 ga watan Yuni, 2025.

’Yan sanda sun ce waɗanda ake zargin sun yi amfani da makamai masu hatsari kamar bindiga, adda, takobi da man fetur.

Dukkanin mutum 20 da ake tuhuma sun ce ba su da laifi.

Bayan sun bayyana matsayinsu, lauyan ’yan sanda ya roƙi kotu da ta tura su gidan yari tare da ɗage shari’ar zuwa wani lokaci.

Lauyan da ke kare su ya nemi a ba da belinsu, amma lauyan gwamnati ya ce bai da isasshen lokaci don ya amsa wannan buƙata bisa doka.

Alkalin kotun, Mai shari’a Boniface Ngyong, ya ce ba za a saurari buƙatar belin a yanzu ba, saboda ƙorafin da lauyan gwamnati ya gabatar.

Ya ɗage shari’ar zuwa ranar 13 ga watan Agusta, 2025, sannan ya umarci a ci gaba da tsare su a gidan yari na Jos.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure yan sanda su ɗaurin aure gurfanar da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
  • Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati