Leadership News Hausa:
2025-10-15@05:57:25 GMT

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

Published: 12th, July 2025 GMT

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

An dai yi ta tsokaci kan cewa ko Obi zai amince da mukamin mataimakin shugaban kasa tare da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, kamar yadda ya yi a 2019.

Obi ya ce, “Takarar shugaban kasan Nijeriya zan yi a 2027, kuma na tabbatar da cancanta.”

A kan ko zai hakura ya zama mataimakin takarar Atiku a 2027, Obi ya bayyana cewa, “Wannan abun wasa ba ne, babu wanta ya tattauna hakan.

Mutane ne kawai yin irin wannan tunani. Amma a zahirin gaskiya babu wanda ya bayyana hakan.”

Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya kuma jaddada cewa har yanzu yana shi mamba ne a jam’iyyar LP.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa Obi yana daga cikin shahararrun mutane a cikin hadakar ADC da ‘yan adawar masu kokarin karbe mulki a wurin Shugaban kasa Bola Tinubu na jam’iyyar APC, wanda ke neman zarcewa a wa’adi na biyu a zaben 2027.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: takara

এছাড়াও পড়ুন:

Rasha ta kai wa tawagar kayan agajin MDD hari a Ukraine

Rasha ta kai harin jirage kan ayarin kayan agajin Majalisar Dinkin Duniya a makwabciyarta kasar Ukraine da suka fi shekara biyu suna yaki.

Hukumomin Ukraine sun dakarun soji da ke yankin kudancin Kherson da suka mamaye a Ukraine ne suka kai harin a ranar Talata, inda suka lalata motocin Shirin Abinci na Duniya, a yayin da ma’akatan agajin suka shafe kimanin awa hudu ba su motsa ba saboda luguden bamabaman.

Kwamandan hukumar soji da ke yankin ta bayyana cewa an kona motoci hudu tare da lalata wata a cikin tawagar kayan agajin, amma ba a samu asarar rayuka ba a harin da aka kai da jirage marasa matuka da manyan bindigogin atilare a garin Bilozerka.

Ministan Harkokin Wajen Ukraine, Andriy Sybiga ya bayyana harin a matsayin “wani mummunan karya dokokin kasa da kasa, wanda ke tababtar da cewa Rasha ba ta mutunta rayukan fararen hula da nauyin da ya rataya a wuyanta na kasa da kasa.”

Shugaban Hukumar Zaɓen Yobe Jihar Yobe ya rasu Issa Bakary Tchiroma ne ya lashe zaɓen Kamaru —’Yan adawa

Kawo yanzu dai Majalisar Dinkin Duniya ko Rasha ko Amurka ba su ce uffan kan lamarin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC
  • ’Yan Majalisar Tarayyar Kaduna 3 sun sauya sheka zuwa APC
  • Rasha ta kai wa tawagar kayan agajin MDD hari a Ukraine
  • Shugaban Hukumar Zaɓen Yobe Jihar Yobe ya rasu
  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
  • An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta