Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da kai hare-hare a yankuna daban-daban na Gaza, kuma Falasdinawa da dama sun yi shahada

Jiragen yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila sun ci gaba da ruwan bama-bamai a yankuna daban-daban na zirin Gaza a rana ta 117 da yakin ya yi sanadiyar shahadan Falasdinawa da dama.

A cewar majiyoyin kiwon lafiya, sama da Falasdinawa 45 suka yi shahada tun daga wayewar garin Juma’a a zuwa safiyar yau a yankuna daban-daban na zirin Gaza.

Yousuf Al-Zaq, wanda aka bayyana shi a matsayin fursuna mafi ƙanƙanta bayan mamayar da aka kai wa gidansa da ke kan titin Al-Thawra a tsakiyar Gaza ya yi shahada.

An haifi Yousuf a cikin gidan yarin Isra’ila a shekara ta 2008, kuma sunansa yana da nasaba da labarin mahaifiyarsa, ‘yar fursuna Fatima Al-Zaq, wacce ta haife shi a gidan kurkuku.

Fararen hula 4 ne suka yi shahada yayin da wasu goma suka jikkata sakamakon harin bam da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan wani gida da ke kan titin Jaffa a unguwar Tuffah da ke gabashin birnin Gaza.

Kanun labarai

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

Sojojin Nijeriya sun kashe wani kwamandan ƙungiyar ƴan ta’adda IPOB/ESN da ake nema ruwa a jallo, mai suna ‘Alhaji’, tare da wasu mutane 26 a jerin hare-haren da suka kai a sassan ƙasar tsakanin 8 zuwa 11 ga Oktoba, 2025. Rundunar Sojin ta ce an kuma ceto mutane biyar da aka yi garkuwa da su, tare da kwace makamai, da harsasai, da kuɗaɗe.

A kudu maso gabas, Sojojin Operation UDO KA sun kai farmaki a Izzi, jihar Ebonyi, inda suka kashe ‘Alhaji’ bayan ya yi yunƙurin kwace bindiga daga hannun wani Soja lokacin kama shi. Haka kuma, a jihar Imo, an rusa wata maboyar IPOB/ESN da ake amfani da shi wajen horar da mambobi.

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

A Arewa maso gabas, Sojojin Operation Haɗin Kai sun kashe ‘yan ta’adda tara a Magumeri da Gajiram a jihar Borno, inda suka ceto fararen hula biyu tare da ƙwato fiye da Naira ₦4.3 miliyan. A wasu hare-haren sama a jihar Sokoto, an hallaka shugabannin ‘yan ta’adda da dama, yayin da aka kama masu safarar miyagun ƙwayoyi daga Legas zuwa Zamfara.

A Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Kudu, Sojojin Operation Whirl Stroke da Operation DELTA SAFE sun kama masu garkuwa da mutane, sun kashe ‘yan ƙungiyar asiri biyu, kuma sun ƙwato makamai da babura. Rundunar Sojin ta ce gaba ɗaya an kashe ‘yan ta’adda 26, an kama mutum 22, kuma an ceto mutane biyar da aka yi garkuwa da su.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato October 11, 2025 Tsaro Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno October 11, 2025 Tsaro Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 
  • Sojojin Madagaska sun karbe mulkin kasar
  • Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila
  • Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
  • Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza
  • Falasdinawa Sun Gano Gawakin Wadanda HKI Ta Kashe A gaza  Fiye Da 320 Cikin Kwanaki Biyu Kacal
  • Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
  • Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon