Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta
Published: 23rd, July 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa; Ba zai yiwu Iran ta iya yin watsi da shirinta na inganta sinadarin Uranium ba
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Har yanzu ba a daina sarrafa sinadarin Uranium ba a Iran, duk da irin barnar da hare-haren Amurka ya yi wa cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran.
A wata hirarsa da Fox News, Araqchi ya amsa tambayoyi kan cewa: “Shin shirin inganta sinadarin Uranium a Iran ya dawo? Shin har yanzu yana ci gaba, ko kuma barnar da aka yi wa Iran ya yi tsanani har ta kai ga dakatar da shi gaba daya?” Araqchi ya amsa da cewa; “Ba a daina bainganta sinadarin ba, duk da cewa barnar ta yi tsanani, amma duniya ta sani Iran ba za ta iya yin watsi da shirinta na inganta sinadarin Uranium ba saboda muhimmancinsa, domin wannan nasara ce ta masana kimiyyar kasar, kuma a halin yanzu abin alfahari ne ga kasa, kuma inganta sinadarin Uranium yana da matukar muhimmanci ga Iran.”
Da yake amsa tambayar cewa: “Mene ne dalilin da ya sa Iran ba za ta shigo da sinadarin uranium da ake inganta shi daga waje ba kamar yadda wasu kasashe ke yi? Araqchi ya ce: “Saboda wannan nasara ce ta ilimi, nasara ce da kasar Iran ta samu, to me ya sa za mu shigo da shi daga waje, duk da za ta iya samar da kanta?”.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: inganta sinadarin Uranium
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
Jami’in harkar shari’ar kasa da kasa ya bayyana cewa: Harin da aka kai wa Iran babban laifi ne kuma jarrabawa ce ta tarihi ga kwamitin sulhu
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan harkokin shari’a da kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya ce: Harin da aka kai wa Iran babban laifi ne, kuma jarrabawa ce ta tarihi ga kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya.
A yayin wani taron manema labarai da ya yi da wakilan kasashe mambobin Majalisar Dinkin Duniya fiye da 110 a birnin New York na kasar Amurka a jiya Litinin, Gharibabadi ya bayyana ma’auni na wuce gona da iri da gwamnatin yahudawan sahayoniyya da Amurka suka dauka kan yankin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma sakamakonsa ga zaman lafiya da tsaro a duniya.
Ya dauki gwamnatin yahudawan sahayoniya a matsayin babbar mai haifar da rashin tsaro da zaman lafiya a yankin cikin shekaru 80 da suka gabata, yana mai jaddada cewa: Wannan ita ce gwamnatin da ya zuwa yanzu ta aiwatar da ayyukan ta’addanci sama da 3,000, tare da raba Falasdinawa sama da miliyan bakwai da muhallansu, da kashe dubban daruruwan Falasdinawa, tare da kame Falasdinawa sama da miliyan guda.