Aminiya:
2025-10-15@22:54:39 GMT

Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m da bindigogi a hanyar Jos

Published: 12th, July 2025 GMT

Sojoji sun kama wani ƙasurgumin mai garkuwa da mutane ɗauke da tsabar kuɗi Naira miliyan 13 a kan hanyar Kaduna zuwa Jos a Jihar Kaduna.

Dakarun Rundunar Operation Safe Haven sun kuma ƙwace bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da harsasai 30 a hannun ɗan ta’addan a  Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna.

Kakakin rundunar, Manjo Samson Zhakom, ya ce dubun ɗan ta’addan ta cika ne a wani shingen bincike da ke yankin Agameti a kan babbar hanyar Wamba zuwa Jos.

Manjo Zhakom ya ce a ranar Laraba, sojoji suka tsayar da wata mota ƙirar Volkswagen Golf da ke ɗauke da mutum uku, amma kafin ta ƙaraso inda za ta tsaya, biyu daga cikin mutanen suka fice suka tsere.

Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa

Ya bayyana cewa sojojin sun gano ramin harbin bindiga da kuma jini a jikin motar, kuma direban ya yi yunƙurin ba su cin hanci amma suka ƙi karba.

“Suka kama shi, bayan cikar wanda ake zargin da kuma cikin motar suka gano bindigogi biyu ƙirar AK-47 da harsasai 30 da wayoyi guda uku da layu da tsabar kuɗi N13,742,000, da wuƙa da sauransu.

“A yayin bincike ya amsa cewa yana da hannu garkuwa da mutane a kan hanyar Jos zuwa Makurɗi, kuma ya amince ya kai sojoji maɓoyarsa.

“A yayin da suke tafiya, wanda ake zargin ya yi yunƙurin ƙwace makamin jami’anmu, amma suka murƙushe shi” in ji shi.

Manjo Zangon ya ce rundunar na ci gaba da zurfafa bincike domin kamo sauran ’yan ta’addan da kuma tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Harsasai

এছাড়াও পড়ুন:

Ba za mu yi sulhu da ’yan bindiga ba sai sun yi tuba na gaskiya — Radda

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda, ya sake jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta yi sulhu da ’yan ta’adda ba waɗanda ke kashe mutane ba gaira ba dalili.

Gwamnan, ya bayyana hakan ne a yau a wajen bikin yaye sabbin jami’an tsaron cikin gida (Community Watch Corps – CWC) guda 100, a karo na uku da aka gudanar a Katsina.

Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Radda, ya karyata rahotannin da wasu kafafen yaɗa labarai suka yada cewa gwamnatinsa tana tattaunawa da ’yan bindigar da ke ɓoye a dazuka.

A cewarsa: “Babu wata tattaunawa ko sasanci da gwamnati ke yi da ’yan ta’adda. Wadannan labarai ƙarya ne, kuma manufar gwamnati ita ce kawo ƙarshen ta’addanci, ba yin sulhu ba.”

Sai dai ya ce, gwamnati za ta iya rungumar zaman lafiya idan waɗannan mutane sun yi tuba na gaskiya, tare da miƙa wuya, suka daina zubar da jini.

Gwamna Radda, ya bayyana cewa horar da jami’an CWC wani ɓangare ne na sabuwar dabarar gwamnati ta inganta tsaro, musamman a yankunan karkara da suka fi fama da hare-haren ’yan ta’adda.

Tun bayan ƙaddamar da Katsina jami’an tsaron a shekarar 2023, an horar da dubban matasa sama da 2,400 daga sassa daban-daban na jihar.

Wadannan jami’ai na aiki tare da ’yan sanda, sojoji, da jami’an Sibil Difens, don taimakawa wajen samun bayanan sirri da hana hare-haren ’yan ta’adda.

Gwamnan, ya ce horar da waɗannan jami’ai zai taimaka wajen kawo ƙarshen satar mutane da hare-haren ’yan bindiga, tare da tabbatar da zauna lafiya a Jihar Katsina.

Ya kuma yi kira ga al’umma su bai wajami’an tsaro haɗin kai, su rika bayar da bayanai domin ganin an samu nasara a yaki da ta’addanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba za mu yi sulhu da ’yan bindiga ba sai sun yi tuba na gaskiya — Radda
  • Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako
  • An kama mata da miji suna safarar makamai a Kaduna
  • ’Yan bindiga sun kai hari a Kankia
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
  • ’Yan Majalisar Tarayyar Kaduna 3 sun sauya sheka zuwa APC
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno