HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi
Published: 23rd, July 2025 GMT
Gwamna Bala Muhammad ya ƙaddamar da aikin gyare-gyare da sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi kan kuɗin da ya haura Naira biliyan bakwai, wanda ya haɗa da inganta kayan aiki, ofisoshi, da kuma gina sabon ofishin hukumar kula da harkokin majalisa.
A yayin ƙaddamarwar da aka gudanar ranar Talata, Gwamna Bala ya bayyana cewa wannan gyara na cikin shirin gwamnatinsa na sauya fasalin birane da samar da muhalli mai kyau ga ma’aikata domin sauƙaƙa aikinsu.
Ya ƙara da cewa tuni aka riga aka biya rabin kuɗin aikin domin tabbatar da cewa aikin ya kammala a kan lokaci.
Kwamishinan gidaje da muhalli, Danlami Ahmed Kawule, ya ce aikin zai ƙunshi gyaran zauren majalisar, ofisoshin mambobi, gina sabbin hanyoyin ruwa da wutar lantarki na masu amfani da hasken rana, da kuma gyara titunan cikin majalisar.
Tun da farko, mambobin majalisar sun koma ofishin tsohon mataimakin gwamna domin ci gaba da aikinsu yayin da ake gudanar da gyaran.
Gwamnan ya yaba wa fahimtar da ke tsakaninsa da majalisar, yana mai cewa hakan ne ke bai wa gwamnati damar aiwatar da ayyukan ci gaba.
Kakakin Majalisar, Abubakar Y. Suleiman, ya bayyana godiya bisa wannan ci gaba, yana mai cewa haɗin kai tsakanin majalisar zartarwa da majalisar dokoki na taka muhimmiyar rawa wajen kawo ci gaba a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Dokokin Bauchi
এছাড়াও পড়ুন:
An wajabta wa ɗaliban firamare mallakar lambar NIN a Bauchi
An wajabta wa ɗaliban makarantun firamare da Ƙaramar Sakandare mallakar lambar shaidar zama ɗan ƙasa (NIN) a Jihar Bauchi.
Hukumar Kula da Ilimin Bai-ɗaya a Matakin Farko ta jihar (SUBEB) ce ta bayar da umarnin ta hannun shugabanta, Alhaji Adamu Mohammed Duguri.
Ya bayyana cewa mallakar lambar NIN ta zama tilas lura da duk hukumomin shirya jarabawa da manyan makarantu suna amfani da ita kafin yi wa ɗalibai rajista.
Ya umarci shugabannin makarantun firamare da sakandare da su umarci ɗalibansu da su tabbata sun yi rajistar katin shaidar ɗan ƙasa sun mallaki lambar NIN kafin shekarar da za su zana jarabawar kammala makarantar da suke.
NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki SanusiHaka zalika ya buƙaci da su tabbatar ’ya’yansu sun mallaki lambar NIN kafin su kai aji 6 na firamare zuwa aji 3 na Ƙaramar Sakandare domin guje wa makara.
Haka kuma ya umarci Sakatarorin Ilimi na ƙananan hukumomin jihar su tabbatar an bi wannan umarni sau da ƙafa domin guje wa fafar hira a ranar tafiya.