Dakarun juyin jaya halin Musulunci ta Iran sun kama wani wakilin hukumar leken asirin Isra’ila Mossad a arewacin kasar Iran

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci sun sanar da kame wani jami’in hukumar leken asirin haramtacciyar kasar Isra’ila “Mossad” a lardin Mazandaran (arewacin kasar Iran), wanda ke shirin kai harin ta’addanci a cikin kasar.

Sanarwar da dakarun kare juyin juya halin suka fitar ta bayyana cewa: wani ma’aikacin fage na makiya da ke shirin aiwatar da ayyukan ta’addanci ta hanya kai tsaye wajen jagorantar masu adawa da Iran a kasashen waje, an kama shi ne a wani gagarumin samame da jami’an leken asirin na Karbala suka kai, kafin ya aiwatar da duk wani aikin ta’addanci.

Sanarwar ta kara da cewa: Bincike ya kai ga gano tare da kama wasu da dama daga cikin ‘yan kungiyar leken asirin da lamarin ya shafa.

Tawagar masu leken asiri ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci a lardin Mazandaran ta tabbatar da cewa tana cikin shiri da kuma taka tsantsan, kuma ta yi gargadin cewa “duk wani mataki na nuna adawa da tsaron kasar, zai fuskanci dauki mai tsauri da raɗaɗi.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Aref Ya Bayyana Cewa: Iran Ba Ta San Kalmar Mika Wuya Ba A Al’adunta Da Tsaronta

Mataimakin shugaban kasar na farko ya jaddada cewa: Kalmar “mika kai” ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron Iran

Mataimakin shugaban kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya jaddada cewa: kalmar mika wuya ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron kasar.

Arif ya ce: Kamar yadda kuke gani kalmar “mika kai” ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yana mai jaddada cewa, su mutane ne masu wayewa, tare da ingantaccen tarihin al’adu wanda ya wuce dubban shekaru. Ba su neman yaki, kuma ba su fara shi ba. Sun yi imani da zaman lafiya da kwanciyar hankali, kuma a shirye suke don tattaunawa, amma ba za su mika wuya a kowane hali ba.

A wata hira da ya yi da KHAMENEI.IR, Aref ya jaddada cewa: An sha ambaton hakan, sannan kuma Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa ba za mu fara yaki ba, amma idan aka tsokani Iran, to Iran zata mayar da martani, kuma haka yake har yanzu. Maƙiya ‘yan sahayoniyya ba za a taba amince da su ba. An dai tsagaita bude wuta a kasar Labanon, amma kamar yadda ake gani bayan tsagaita wuta an samun adadin shahidai masu yawa. Sadaukarwarsu ta kasance domin kare Iran ce.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kyautar ‘Jakadan Abota’ Na Kasar China Ya Shiga hannun Iran
  • Kamfanonin Jiragen Ruwa Sun Yanke Hulda Da Isra’ila Saboda Matsalar Hare-Haren Kasar Yemen
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Jagora Da Kansa Ya Shiga Dakin Ba Da Umarnin Sojin Lokacin Yaki
  • Aref Ya Bayyana Cewa: Iran Ba Ta San Kalmar Mika Wuya Ba A Al’adunta Da Tsaronta
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana cewa: Martanin Da Iran Ta Mayar Ne Ya Sanya Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta
  • Kwamandan Sojin Iran Ya Jaddada Kare Kan Iyakokin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci  ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
  • Babban Kwamandan Sojin Iran Ya Bayyana Cewa Iran Ta Koyawa Gwamnatin Isra’ila Hankali
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran