An tsara Jirgin zai rinka yin zirga-zirga ne, zuwa daukacin kasashen da ke Afirka ta yamma da kuma sama da haka, musamman yin zirga-zirga daga Nijeriya zuwa kasashen, Jamhiriyar Benin, Togo, Ghana, Kamaru, Sierra Leone, Ibory Coast, Masar, Afirka ta Kudu da sauransu, tare da kuma nuna bukatar yin kasuwanci wadda tuni, aka fara ta.

A martaninsa kan wannan nasarar, Shugaban Hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho ya bayyana cewa, “ Wannan nasarar ta nuna irin mayar da hankalin da NPA ke ci gaba da yin a kara bunkasa ayyukan Hukumar wanda ta zo daidai da ta irin ma’aikatar bunkasa tattalin arzikin kasa.

A na ta bayanain Mataimakiyar Shugabar kamfanin na On her Clarion Shipping West Africa Limited, Bernadine Eloka, ta bayyana cewa, jigilar kaya a cikin Jirgin a Tekunan ruwan Nijeriya da kuma kokarin kara karfafa hada-hadar kasuwanci a Afrika ta yamma, za ta taimaka matuka wajen kara habaka kasuwanci.

Ta ce, manufar kamfanin shi ne, ya kara samar da saukin yin hada-hadar zirga-zigar kaya a tsakanin kasashen Afirka, musamman ta hanyar bude sabon babin kasuwanci a Tashoshin Jirgan Ruwa na Nijeriya da kasashen, Ghana, Ibory Coast da kuma sama da haka.

“Mun samar da Jirgin na MB Ocean Dragon ne, domin mu samar da saukin ga yin jigilar Kwantainoni, mai makaon yin jigilarsu, a kan tituna,” Inji ta.

Ta ci gaba da cewa, mai makon a rinka shan wahala wajen yin jigilar Kwantainoni a cikin manyan motoci daga Tashar Jirgin Ruwa ta Lekki zuwa ta Onitsha, Fatakwal, ko kuma Kalaba, Jirgin na Dragon, zai iya dakon Kwantainonin da suka kai yawan 349 ya kuma kaisu, Tashar Jirgin Ruwan da ka tsara za a kaisu, a cikin kwana biyu.

A cewarta, wannan Jirgin zai kuma taimaka wajen kara karfin guiwar sauran masu zuba hannun jari a fanin, samar da ayyukan yi da kuma rage dogaro kan Jiragen Ruwa na ketare.

Shi kuwa Manajin Darakta na mai kula da sashen kaya na kamanin Mustafa Mohammed, ya bayyana cewa, kamfanin ya mayar da hankali wajen yin gasa da sauran manyan kamfanonin kasashen duniya kamar su, Maersk Line da MSC, wanda hakan ya sanya, kamfanin ya fara turo Jirginsa na MB Ocean Dragon, zuwa cikin Nijeriya, musamman domin ya zuba hannun jarinsa a fannin sufurin Jiragen ruwan kasar.

Ya ci gaba da cewa, tuni kamfanin ya samu wasu kamfanoni da ke bukatar a yi masu dakon Kwantainoni guda 1,300, musamman wasu manoma da ke son ayi masu jigilar amfanin gona da kuma wasu masana’antu da ke bukatar a yi masu jigilar kayan da suka sarrafa, domin kar su su samu jinkirib, da zai haifar masu da yin asarar kayansu.

Kazalika, wannan ci gaban dai, na zuwa ne, daidai da sanarwar da Shugaban NPA Dakta Abubakar Dantsoho ya yi, na zuba dala miliyan 60 a matsayin sabon hannun jari, domin a kara samar da huddar cinikayya, ta kara bunkasa harkokin kasuwanci a Tashoshin Jiragen ruwa na kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Shi ma Uban taro mai masaukin baki, shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya bayyana a jawabinsa na taron kolin cewa, “Idan har ba a samu sauyi a tsarin gudanar da harkokin kasa da kasa a wannan karni na 21 ba, to ya zama wajibi kasashen BRICS su taimaka wajen ganin an sabunta shi.”

BRICS taska ce ta hadin kai, daidaito da kuma kokarin tafiya tare don samun ci gaba da tsira tare, da kuma karfafawa kasashe masu neman ‘yancin fadin albarkacin bakinsu a harkokin tsare-tsare na hadin kan kasashen duniya.

Taron kolin kungiyar na bana, na zuwa ne a daidai lokacin da kasuwannin duniya ke cike da firgici biyo bayan yakin cinikayya da kasar Amurka ta kaddamar, amma BRICS ta tsaya tsayin daka wajen inganta harkokin tattalin arziki, inda kungiyar ke samar da wani dandali na bai daya da ke tallafawa cinikayya a kasashe daban-daban, da inganta cinikayyar a tsakaninsu, wanda hakan ya ba su damar bunkasa amfani da kudaden cikin gida, don rage dogaro kan wasu kasuwanni masu iyaka.

Yayin da kasashe da dama ke nuna sha’awar shiga kungiyar, hakan na nuni da tasiri da nasarar da kungiyar ke samu cikin sauri, saboda ta bayyana gaskiya da adalci a fili, ta inganta tsarin dimokuradiyyar duniya, kowa yana da ‘yancin fadi a ji.

 

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanonin Jiragen Ruwa Sun Yanke Hulda Da Isra’ila Saboda Matsalar Hare-Haren Kasar Yemen
  • Mayakan Huthi Sun Kara Kai Wasu Hare-Hare da Makamai Masu Linzami Kan BenGurio
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Hadin Gwiwar Hukumar Kwastam Don Farfado Da Yankin Kasuwanci Na Maigatari
  • Babban Kwamandan Sojin Iran Ya Bayyana Cewa Iran Ta Koyawa Gwamnatin Isra’ila Hankali
  • Yemen Ta Nutsarda Wani Jirgin Ruwana HKI Saboda Sabawa Haramcin Wucewa Ta Red Sea
  • Sojojin Yemen Sun Nutsar Da Jirgin Ruwan “Eternity” Dake Hanyar Zuwa HKI
  • Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki
  • Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
  • Kwanan nan gwamnati za ta sake kara kudin lantarki a Najeriya – Minista