Leadership News Hausa:
2025-10-15@12:21:26 GMT

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

Published: 11th, July 2025 GMT

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran kayayyakin da aka raba sun haɗa da irin shinkafa kilogiram 34,800, irin masara kilogiram 80,000, da lita 23,740 na maganin ciyawa, lita 11,735 na maganin kwari, da buhunan sinadarai na gyaran iri 23,470.

 

A yayin jawabin maddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana cewa rabon takin zamani kyauta na nuni da yadda gwamnatinsa ke ƙoƙarin kawo sauyi a jihar Zamfara ta hanyar noma mai ɗorewa da bunƙasa karkara.

 

Ya ce, “Aikin noma shi ne ginshiƙin tattalin arzikin jiharmu, ba sashe kaɗai ba ne, amma asalin al’ummarmu ne.

 

“Gwamnatinmu ta rungumi taken ‘noma abin alfaharinmu ne’. Noma na nuna ainihin ko su wane ne mu da kuma abin da ya kamata mu ba da fifiko a matsayinmu na al’umma, sama da kashi 85 na al’ummarmu sun dogara ne kan noma don rayuwa. Haƙƙin ne a kan mu, kuma haƙiƙa ya zama wajibi mu ba su goyon baya da ƙarfafa su.

 

“Wannan gwamnatin tana kallon noma a matsayin dabarar samar da abinci, samar da ayyukan yi, rage fatara, da bunƙasar tattalin arzikin ƙasa baki ɗaya, shi ya sa muke aiwatar da shirin kawo sauyi a fannin noma, wanda ya dace da buƙatun al’ummominmu da kuma yin daidai da manufar ci gaba mai ɗorewa ta 2, wanda ke neman kawo ƙarshen yunwa, inganta abinci mai gina jiki, da bunƙasa noma mai ɗorewa.

 

“Duk da ƙalubalen sauyin yanayi da kuma ƙarshen lokacin damina na 2025, mun ci gaba da mai da hankali sosai, gwamnatinmu tana tallafa wa manoma da kayan aikin da ake buƙata don bunƙasa noma da samun kuɗin shiga, muna saka hannun jari a fannin samar da iri, takin zamani, fasaha, da jarin bil’adama don samun tasiri na dogon lokaci.

 

“Manufarmu ta haɗa da ƙarfafa mata, matasa, da kuma ɗaiɗaikun mutane masu buƙatu na musamman a matsayin wakilai na kawo sauyi, ba wai mahalarta kaɗai ba. Mun bullo da ingantaccen tsarin rabo cikin gaskiya don tabbatar da cewa tallafin ya isa ga manoman da suka dace a daidai lokacin da ya dace.

 

“Mun gane cewa manoma na fuskantar matsaloli kamar rashin damar samun kayan aiki, kuɗaɗe, rashin tabbas na kasuwa, asarar bayan girbi, da kuma tasirin sauyin yanayi. Amma muna tunkarar waɗannan batutuwa.

 

“Ta hanyar shiga tsakani, muna gina tsarin da zai taimaka wa manomanmu daga shuka har zuwa bayan girbi. Muna haɓaka noma da injinan zamani.

 

“Bari na dan ɗauki lokaci in yi magana kai tsaye ga waɗanda suka ci gajiyar shirin na bana. Waɗannan kayayyakin ba na sayarwa be ne. Ba kayayyakin da za a yi ciniki da su ba ne domin a samu ci gaba cikin gaggawa. Kayan aiki ne na samar da ci gaba, zuba jari a nan gaba da kuma makomar Zamfara. Ku yi amfani da su cikin hikima, ku yi amfani da su cikin gaskiya, ku bar su su zama ginshiƙi na ƙaruwar girbi da inganta rayuwa.

 

“Baƙin alfarma, ’yan uwa maza da mata, yanzu ya zama abin alfaharina na ƙaddamar da shirin Rarraba Kayayyakin Aikin Noma na 2025 a hukumance, wanda zai amfani ƙananan manoma 59,205 a faɗin jihar mu.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka

Kasashe hudu da suka fi kokari a cikin wadanda suka kare a mataki na hudu za su fafata wasannin raba-gardama, sai wadanda suka samu nasara su sake raba-gardama da wasu kasashen na waje.

 

A yanzu daI manyan kasashen nahiyar ta Afirka irin su Kamaru da Nijeriya suke fuskantar barazanar rasa gurbi, duk da haka suna da wasu damarmakin da idan suka yi sa’a za su iya tsintar kansu a gasar a badi.

 

Kasar Masar ta wuce Burkina Faso da maki biyar, sannan idan ta samu nasara a kan Djibouti shikenan ta samu tikiti. Ita kuma kasar Djibouti tana can karshen teburi ne, domin maki daya tak take da shi a wasa takwas da ta buga.

 

Idan ma Masar ta yi rashin nasara a wasan, za ta fatata da Guinea-Bissau a ranar Lahadi. Burkina Faso kuma wadda take kokarin zuwa ta biyu za ta buga wasa ne da kasar Saliyo, sai kuma kasar Habasha, amma tana bukatar samun nasara a wasannin kafin samun gurbin buga wasannin raba-gardama.

 

A rukunin (B) kuwa nasarar da Senegal ta samu a kan DR Congo ce ta ba ta damar darewa teburin rukunin, inda yanzu ta ba da tazarar maki daya. Tawagar ta Teranga Lions za ta je wasa da Sudan ta Kudu wadda ke karshen teburi, sai ta buga wasan karshe da Mauritania, inda take bukatar nasara biyu domin samun shiga gasar.

 

DR Congo dai na fatan Senegla ta yi rashin nasara, ita kuma ta samu nasara a wasannin biyu a gidan Togo da kuma Sudan a gida. Sudan na bukatar nasara a duka wasanninta, sannan Senegal ta yi rashin nasara wasanninta biyu domin samun gurbin zama ta daya a teburi, amma tana da damar zuwa ta biyu idan ta doke Congo.

 

A wannan rukunin kuma bayan hukuncin da FIFA ta dauka a kan kasar Afirka ta Kudu na cire mata maki uku saboda sanya dan wasan da bai cancanta ba a wasanta da kasar Lesotho.

 

Yanzu Benin ce kan gaba a rukunin, inda take saman Afirka ta Kudu da bambancin kwallaye, sai Nijeriya da Rwanda suke da maki da na hudu, amma duk suna da damar samun gurbi.

 

Benin na da wasa a gidan Rwanda da Nijeriya, sai tawagar Afirka ta Kudu za ta buga da Zimbabwe, sai Rwanda a gidanta. Nijeriya tana da wasa a gidan Lesotho sai Benin, kuma dole ne ta ci wasanninta guda biyu, amma ko da ta lashe wasannin, sai yadda ta wakana a sauran wasannin kafin sanin matsayarsa.

 

Nasarar da Cape Berde ta samu a kan Kamaru da ci daya mai ban haushi a watan jiya ta sa kasar ta kama hanyar kafa tarihin zuwa gasar cin Kofin Duniya na farko a tarihinta.

 

Yanzu kasar na bukatar nasara daya kacal a wasanta da Libya ko kuma a wasanta a gida da kasar da ke karshen teburi, wato tawagar ‘yan wasan kasar Eswatini. Kamaru za ta iya samun nasara da bambancin zura kwallaye idan ta doke Mauritus da Angola, ita kuma Cape Berde ta yi canjara a wasannin biyu, ko kuma idan Kamaru ta samu maki hudu a wasannin biyu,

 

ita kuma Cape Berde ta yi rashin nasara. Sai kuma Libya ce ta uku, kuma maki uku ne tsakaninta da Kamaru, kuma za ta iya bayar da mamaki.

 

Kasar Morocco ta riga ta samu gurbin shiga gasar cin kofin duniyar.

 

A cikin rukuni na E kuma kasashen Tanzania da Nijar da Zambia ne sauran kasashen da ke rukunin, kuma yanzu suna ta fafatawa ne domin samun gurbi na biyu wanda zai iya buga wasan raba-gardama.

 

A cikin rukuni na (F) kuwa, Ibory Coast na gaba da Gabon da maki daya bayan canjaras da ta yi da kasar Gabon a Francebille a watan Satumba. Kasar za ta je gidan Seychelles a ranar Juma’a, sai kuma ta fafata da Kenya a ranar Talata. Gabon za ta je gidan Gambia, sai kuma Burundi ta bakunce ta.

 

A cikin rukuni na G kuwa Algeria ita ma ta ba da tazarar maki hudu a saman teburi, kuma tana bukatar maki uku ne a wasanta da kasar Somalia wadda ta riga ta fita ko kuma ta biyu Uganda zai ta ba gurbi. Uganda ta zarce Mozambikue ne kawai da bambancin zura kwallo a matakin na biyu.

 

Can kuwa a cikin rukuni na H, Tunisia ta riga ta tsallake bayan samun gurbi duk da cewa akwai sauran wasaNNI biyu da za ta buga, inda ita kuma Namibia ta dage wajen neman zama ta biyu a rukunin. Namibia za ta je gidan Liberia a ranar Alhamis kafin ta karkare a birnin Tunis.

 

Daga rukuni na I kuma kasashe uku ne ke fafutikar samun gurbin na kai-tsaye, amma Ghana ce a sama da tazarar maki uku a saman Madagascar da Comoros. Ghana za ta samu gurbi idan ta yi nasara sannan Madagascar ta gaza samun maki uku. Wasan karshe na Ghana shi ne a gida da Comoros, ita kuma Madagacar za ta je gidan Mali a wasan na karshe.

 

Kamar yadda FIFA ta tsara, kasashe hudu da suka fi maki a cikin kasashen da suka kare a na biyu daga rukunoni tara din ne za su fafata wasannin raba-gardama a watan Nuwamba.

 

Zuwa yanzu dai kasashen Gabon da Madagascar da DR Congo da Burkina Faso ne a gaba a cikin tawagogi na biyu. Sakamakon za su iya canjawa bayan wasanni biyu na karshe, sannan kuma ba a riga an sanar da tsarin wasannin na raba-gardama ba.

 

Amma kasashen da suka samu nasara a wasannin na raba-gardama ne za su sake fafatawa a wasanin na raba-gardama da wasu kasashen na duniya kafin samun gurbi a gasar ta duniya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola October 12, 2025 Wasanni Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0 October 9, 2025 Wasanni Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane October 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Kano Na Aikin Gyaran Cibiyoyin Lafiya Da Za Su Yi Gogayya Da Na Ƙasashen Duniya
  • 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako
  • Majalisa ta gayyaci CBN da bankunan kasuwanci kan yawan cire wa kwastomomi kuɗaɗe
  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka