Haɗakar ’yan hamayya alheri ce ga siyasar Nijeriya — Gbajabiamila
Published: 13th, July 2025 GMT
Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnatin Nijeriya, Femi Gbajabiamila ya ce haɗakar ’yan siyasa a jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Nijeriya.
Ya bayyana cewar haɗaka ’yan adawar za ta taimaka wajen hana ƙasar faɗawa cikin siyasar jam’iyyar ƙwaya ɗaya tal.
WFP ya dakatar da tallafin abinci a Yammaci da Tsakiyar Afirka Za a sa zare tsakanin Amurka da Turai kan harajin kasuwanciGbajabiamila ya bayyana haka ne jim kaɗan bayan ya kaɗa ƙuri’arsa a zaɓen ƙananan hukumomin da aka yi a Jihar Legas a jiya Asabar a mazaɓarsa da ke Surulere.
Sai dai tsohon shugaban Majalisar Wakilan ya bayyana shakkunsa kan haɗakar, inda ya ce ce ba ya tunanin za ta yi wani tasirin a-zo-a-gani.
“Muna maraba da samar da haɗakar. Ai ba wannan ba ne karo na farko da aka samu haɗakar ’yan siyasar a wannan ƙasar tamu,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa “a dimokuraɗiyya ana buƙatar hamayya mai ƙarfi, domin idan babu hamayya mai ƙarfi, za mu iya faɗawa siyasar jam’iyyar ɗaya,” in ji shi.
A bayan nan ne dai wasu fitatun ’yan jam’iyyun hamayya ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar da Peter Obi da Nasir El-Rufai da Rotimi Amaechi da sauransu suka ayyana jam’iyyar haɗaka ta ADC domin fuskantar Zaɓen 2027, inda suke fatan za su kayar da Bola Tinubu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: adawa Haɗaka Hamayya
এছাড়াও পড়ুন:
Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya koka bisa yawan bashin da Najeriya ke ciyowa da kuma yadda gwamnati ke facaka da kuɗaɗen.
Sarkin wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) ne, ya kuma bayyana cewa cire tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ta yi shi ne mafi alheri, yana mai cewa da Gwamnatin ba ta cire tallafin mai ba, da Najeriya ta daɗe da tsiyacewa.
“Adawata a ɓangaren shan man ne, saboda muna ba da aikin yi ga matatun mai a Turai. Muna ba da aikin ga masu tace ɗanyen man,” in ji Sarki Sanusi.
Da yake jawabi a Taron Adabi na Duniya na Kano (KAPFEST) da aka gudanar a Kano ranar Asabar, masanin tattalin arzikin ya bayyana cewa ɗabi’ar yawan cin bashin Najeriya za ta yi mummunar illa ga tattalin arzikin ƙasar na tsawon lokaci.
Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Gidauniyar Misilli ta mayar da yara 150 makaranta a GombeMasanin tattalin arzikin ya bayyana damuwa musamman kan yadda gwamnati ke kashe kuɗaɗen da ta ciyo bashin.
Zuwa ƙarshen watan Maris, yawan bashin da ake bin Najeriya ya haura Naira tiriliyan 150.
A yayin taron wanda cibiyar Poetic Wednesdays Initiative (PWI), ta shirya, Sarki Sanusi II ya ce, ya ce, “Ina muke kai wannan tulin bashin da muke ciyowa a ƙasar nan?
“Zan yi farin cikin ganin an yi amfani da kuɗaɗen a fannin ilmantar da matasanmu, saboda su ne za su biya. Amma bai kamata mu yi ciyo bashi muna lafta wa tattalin arzikin ƙasa ba tare da zuba jari a fannin ilmantar da waɗanda su ne za su biya bashin ba.
“Nan da shekara 20 za mu faɗa a matsala a dalikin cin bashi. Dole a zuba jari a fannin inganta rayuwarsu domin samar da abubuwa.”
Ya bayyana cewa Najeriya ba ta yi sa’ar shugabanni nagari ba a tsawon lokaci, yana mai cewa yawancin shugabannin ƙasar ragwage ne masu yawan kawo uzuri.
Sarki Sanusi II ya bayyana kyakkyawan shugabanci a matsayin muhimmin abin da zai ceto Najeriya daga halin da take ciki, wanda ya kira na rashin sa’a.
Da yake sukar yanayin koma-bayan Najeriya alhali wasu ƙasashe sun yi gaba ta fannin kimiyya da fasaha da ci-gaban zamani, Sarki Sanusi II ya buƙaci matsala da su tashi domin karɓar ragamar shugabancin ƙasar, yana mai jaddada cewa hakan abu mai yiwuwa ne idan matasan suka jajirce.