Aminiya:
2025-07-12@19:22:58 GMT

Abin da ya faru tsakani na da DSS bayan kama ni — Ɗan Bello

Published: 12th, July 2025 GMT

Wasu da ake zargin Jami’an Hukumar Farin Kaya (DSS), sun kama fitaccen mai barkwancin nan a kafafen sada zumunta, Bello Habib Galadanci, wanda aka fi sani da Ɗan Bello, a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano.

Sun kama shi ne bayan isowarsa filin jirgin saman, wanda hakan ya jawo hankalin mutane da dama, ciki har da fasinjoji da ma’aikatan filin jirgin.

DSS ta saki Ɗan Bello bayan ta kama shi a Kano Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m a hanyar Jos

Sai dai Ɗan Bello cikin wata hira ta wayar tarho da ya yi da kafar DCL, ya bayyana abin da ya faru, inda ya ce: “Dana sauko wasu mutane wanda kana ganinsu ka san hukumomi ne suka karɓi fasfo da sauran kayayyakina.

“Sai suka ga mota ne na hau mu tafi, ana haka ne sai ga barista Abba Hikima nan, ya zo sai aka yi doguwar magana cikin turanci”, in ji shi.

Ya ƙara da cewa: “Bayan kamar awa ɗaya da rabi sai suka shi kenan za mu iya tafiya. Wannan shi ne abin da ya faru.”

Wasu da lamarin ya faru a idonsu, sun ce suna tunanin jami’an sun zo ne daga Abuja, kuma sun kama Ɗan Bello ba tare da bayyana dalilinsu ba, wanda hakan ya sa mutane da dama cikin ruɗani.

Amma wata majiya ta tabbatar wa Aminiya cewa jami’an sun sako shi bayan ’yan mintuna kaɗan da kama shi.

“Lallai DSS ne suka kama shi, amma sun sake shi daga baya. Wataƙila sun samu sabon umarni ne don a sake shi. Yanzu yana cikin ƙoshin lafiya,” in ji majiyar.

Sai dai Ɗan Bello, ya ce bai yi mamakin kama shi da aka yi bayan isowarsa Najeriya.

“A Najeriya muke. Har da kayan gidan yarina na taho a shirye.

“Ina son mutane su kwantar da hankalinsu, ina lafiya sannan Allah Ya ƙara mana kwanciyar hankali mu saita ƙasarmu, mu ɗora ta a kan hanya wanda ba su fahimci inda aka dosa ba, su fahimta insha’Allah,” a cewar Ɗan Bello.

Ɗan Bello dai, ya yi fice a Arewacin Najeriya, inda yake wallafa bidiyoyinsa na barkwanci da suka kan taɓo batutuwan siyasa da zamantakewa.

Mutane da dama na kallon abubuwan da yake wallafawa a Intanet, inda yake haɗa barkwanci da tsokaci kan abubuwan da ke faruwa a ƙasar nan.

Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomi ba su bayyana dalilin kama shi ba, kuma DSS ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barkwanci Ɗan Bello

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Neja

Aƙalla mutum 13 ne suka rasu, ciki har da ɗan sanda da ’yan sa-kai guda uku, a wani hari da ’yan bindiga suka kai garin Mongoro da ke Ƙaramar Hukumar Mariga, a Jihar Neja.

Harin ya faru ne da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Laraba.

Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna Soludo

Mazauna garin Wamba, sun ce har yanzu suna cikin fargaba saboda ‘yan bindigar ba su bar yankin ba.

A ranar 24 ga watan Yuni, maharan sun kai hari wani sansanin sojoji da ke Kwanan-Dutse, inda suka kashe sojoji 17, tare da jikkata wasu 10.

A cewar wasu mazauna garuruwan, harin na baya-bayan nan ya faru ne a ranar Talata, inda ’yan bindigar suka zo da yawa kuma ɗauke da muggan makamai inda suka yi wa jami’an tsaro da ’yan sa-kai taron dangi.

Sun raunata mutane da dama.

Wani mazaunin yankin wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya ce jami’an tsaron sun yi ƙoƙari, amma alburusansu sun ƙare a yayin artabun, wanda hakan ya sa dole suka ja da baya.

Ya ce ana buƙatar gaggauta tallafa wa ’yan sa-kai a Mongoro saboda yankin na fama da hare-hare.

Wani mazaunin kuma ya ce an kashe mutum 13, ciki har da ’yan sa-kai, sannan ’yan bindigar sun lalata turakun sadarwa, wanda hakan ya haddasa matsalar sadarwa a yankin.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Mariga, Abbas Adamu Kasuwan-Garba, ya tabbatar da harin, amma ya ce ba a tabbatar da adadin waɗanda suka rasu ba tukuna.

Ya ƙara da cewa lamarin tsaro a yankin na ƙara taɓarɓarewa saboda yawan hare-haren da ake kai wa.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar harin, amma ya ce har yanzu babu cikakken bayani.

Saboda tsoron kai hare-haren, manoma da dama a Mariga da Rijau sun daina zuwa gonaki, wasu kuma sun koma birane domin tsira da rayukansu.

Wani mazaunin yankin Rijau, mai suna Ibrahim Ayuba, ya ce mutane da yawa sun tsere daga ƙauyuka zuwa Rijau saboda tsoron kashe-kashe da sace-sacen da ke ƙaruwa a kullum.

A wani yunƙuri na shawo kan matsalar tsaro, Etsu Nupe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jihar Neja, Alhaji Yahaya Abubakar, ya buƙaci haɗin gwiwa da sabbin dabaru domin magance matsalar.

Ya bayyana haka ne yayin da Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Adamu Abdullahi Elleman, ya kai masa ziyara a fadarsa.

Kwamishinan, ya ce manufar ziyarar ita ce ƙarfafa haɗin kai tsakanin sarakuna, al’umma da jami’an tsaro wajen yaƙi da ’yan bindiga da sauran matsalolin tsaro.

Masani ya buƙaci kafa rundunar tsaron daji

Wani masani kan harkar tsaro, Auwal Bala Durumin Iya, ya buƙaci gwamnati ta bai wa ’yan sa-kai da jami’an tsaro makaman da suka fi ‘yan bindiga nagarta.

Ya kuma bayar da shawarar a kafa sabuwar rundunar tsaro domin kula da dazuka, wanda yawancin a can ake aikata laifuka.

Ya ce dole ne a horas da dakarun rundunar sosai, a ba su makamai irin su AK-47, sannan a cire siyasa wajen kula da harkar tsaro.

Ya ce idan aka daina siyasantar da harkar tsaro, aka mayar da hankali kan ƙwarewa, za a iya cimma nasara.

Ya kuma buƙaci gwamnati ta naɗa shugabanni nagari a hukumomin tsaro, tare da tallafa wa ’yan sa-kai da kuɗi da kayan aiki, inda ya yaba wa ƙoƙarinsu duk da cewa ba sa karɓar albashi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DSS ta saki Ɗan Bello bayan ta kama shi a Kano
  • DSS ta kama Ɗan Bello a Kano
  • Jami’an tsaro sun kama Ɗan Bello a Kano
  • Iran:  Goyon Bayan Shugaban Gwamnatin Jamus Ga ‘Yan Sahayoniya, Yin Tarayya Ne A Fada Da Iran
  • Sojoji sun kama mai garkuwa da mutane da bindigogi
  • Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Neja
  • ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna Soludo