Magance Matsalar Yara Da Ba Sa Zuwa Makaranta: Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyarwa A Makarantun Jihar
Published: 11th, July 2025 GMT
A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, ƙaddama da shirin na nuni da ƙwazon gwamnatinsa na yin aiki tare da masu ruwa da tsaki domin aiwatar da dabaru daban-daban na ƙara yawan ɗalibai a makarantun jihar Zamfara.
Ya ci gaba da cewa, “Alƙawarinmu na yin garambawul ya haɗa da tsare-tsare na yaƙi da rugujewar sassan ilimi da samar da haɗin gwiwa, kamar Bankin Duniya ta hanyar shirin AGILE da kuma UNICEF.
“Shirin ciyar da ɗalibai a makarantu da muke ƙaddamarwa a yau, wani bangare ne na shirye-shiryen bayar da agajin gaggawa na inganta rajista da kuma riƙe ɗalibai a makarantu tare da yaƙi da yunwa da rashin abinci mai gina jiki. Wannan baya ga ƙoƙarin mu da wasu ƙungiyoyi masu zaman kansu guda biyu, Cibiyar Ci Gaban Tattalin Arziki ta Ƙasa da Ƙasa da Gidauniyar FINPACT, waɗanda suka amince da tallafa wa gwamnati wajen aiwatar da shirin domin yin aiki a matsayin tushen ilimi.
“A cikin sharuɗɗan, gidauniyar FINPACT za ta ɗauki nauyin ciyar da ɗalibai 1000 a Gusau, Maru, Anka, da Talatar Mafara, yayin da Cibiyar Raya Tattalin Arziki ta Duniya ke ɗaukar nauyin ciyar da ɗalibai 3300 a faɗin Gusau, Talatar Mafara, da Shinkafi.
“Ina kira ga duk masu ruwa da tsaki da sauran hukumomin bayar da agaji da su ƙara binciko hanyoyin samar da ƙarin ayyuka da shirye-shirye, wanda ba wai kawai hakan zai ƙara ƙaimi wajen samar da ilimi mai inganci ba ne, amma zai rage adadin yaran da ba su zuwa makaranta, ta yadda tare za mu mai da jiharmu ta zama abin koyi.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.