Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba
Published: 22nd, July 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Iran ba za ta iya watsi da shirinta na inganta sinadarin Uranium ba
Ministan harkokin wajen na Iran ya fada a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Fox News cewa: Har yanzu ba a dakatar da inganta sinadarin Uranium ba a Iran, duk da irin barnar da aka mata bayan hare-haren da Amurka ta yi mata mai tsanani.
A cikin wata hira da gidan talabijin na Fox News, Araqchi ya ce, “Shin shirin inganta sinadarin Uranium a Iran ya dawo? Shin har yanzu wannan shirin yana ci gaba, ko kuwa barnar da aka yi ta yi tsanani har ta kai ga dakatar da shi gaba daya?” Ya ce: “Ba a dakatar da shi ba, duk da cewa barnar ta yi muni da yawa, amma ba shakka ba za a iya yin watsi da Shirin inganta sinadarin Uranium ba, domin wannan nasara ce ta masana kimiyyar Iran, kuma a halin yanzu abin alfahari ne ga kasar, kuma inganta sinadarin Uranium yana da matukar muhimmanci a gare ta.”
Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa: “Iran ba zata taba matsawa wajen inganta sinadarin uranium da kashi 90 cikin dari ba. Iran ta himmatu wajen tabbatar da samar da makamashin Uranium kasa da kashi 5% domin samar da makamashin nukiliya. Kuma tana inganta sinadarin na Uranium zuwa kashi 20% saboda tana da injin binciken TRR.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: inganta sinadarin Uranium sinadarin Uranium ba
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.