Aminiya:
2025-07-12@02:21:33 GMT

Sojoji sun kama mai garkuwa da mutane da bindigogi

Published: 12th, July 2025 GMT

Sojojin Operation SAFE HAVEN da ke aiki a Arewacin Najeriya, sun kama wani mutum da ake zargi da garkuwa da mutane a kan hanyar Wamba zuwa Jos, tare da kuɗi Naira miliyan 13 da kuma makamai

Wannan kamen ya faru ne a ranar Laraba, 9 ga watan Yuli 2025, a wani shingen bincike da sojoji suka kafa a Agameti, a Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna.

Muna tunanin sayar da matatun man Najeriya — NNPCL Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda

A cewar mai magana da yawun rundunar, Manjo Samson Zhakom, sojojin sun dakatar da wata mota ƙirar Volkswagen mai lamba JJN 336 YZ, ɗauke da mutane uku.

Amma biyu daga cikin su sun tsere kafin a fara bincike.

Bayan duba motar, sojojin sun gano bindigogi biyu ƙirar AK-47, harsashi da yawa, da kuma jini a cikin motar.

Wanda aka kama ya yi ƙoƙarin bai wa sojoji cin hancin kuɗi domin su sake shi, amma suka ƙi amincewa.

Sojojin na ci gaba da ƙoƙarin kamo waɗanda suka tsere domin tabbatar da doka da oda a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mai Garkuwa Da Mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya fadawa shugaban majalisar tarayyar Turai Antonio Costa, kan cewa huldar kasar Iran da hukumar makamashin Nukliya ta duniya IAEA zai kasance tare da sharudda. Saboda hukumar ta yi watsi da ayyukanta na asali ta koma siyasa. Ta fita daga bangaren kwararru ta zama tana bin bukatun wasu.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa dangantakar Iran da hukumar ta IAEA a da can ta zuciya guda ce, bata boyewa hukumar wani abu a cikin ayyukanta na makamashin Nukliya. Amma a halin yanzu mun gano cewa hukumar ce take bawa HKI bayanai dangane da ayyukammu na Nikliya ta kuma bada sunaye dadireshin masana fasahar Nukliya na kasar HKI ta zo ta kashesu kai tsaye ko kuma ta yi amfani da wakilanta a cikin Iran don yin wannan aikin.

Banda haka Hukumar ta rufe idanunta kan shirin makaman Nukliya na HKI gaba daya.  Daga karshe yace Iran zata sauya yadda take hulda da hukumar a lokaci guda tana bin hanyar diblomasiyya don warware matsalolin da suke rage tsakaninta na hukumar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • HKI Ta Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Kan Kudancin Kasar Lebanon
  • Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara
  •  HKI Tana Cigaba Da Yi Wa Mutanen Gaza Kisan Kiyashi
  • Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna Soludo
  • HKI: Sojoji 62 Ne Su Ka Halaka A Gaza A Cikin Wannan Shekara Ta 2025