An kaddamar da shirin koyar da Sinanci mai taken “Hello China”, na gidan rediyon Nijeriya (FRCN), a Abuja babban birnin kasar. Kusan mutane 100, ciki har da jakadan Sin a Nijeriya Yu Dunhai da darakta janar na FRCN Mohammed Bulama ne suka halarci bikin kaddamarwar da ya gudana a jiya Alhamis.

Cikin jawabin da ya gabatar, Yu Dunhai ya ce kaddamar da shirin na koyar da Sinanci da gidan rediyon ya yi, zai samar wa ‘yan Nijeriya wani sabon dandali na koyon harshen Sinanci da fahimtar kasar Sin, tare da samar da kuzari mai dorewa ga hadin gwiwar moriyar juna a fannonin cinikayya da tattalin arzikin tsakanin Sin da Nijeriya

Daga ranar 16 ga wata ne za a fara watsa shirin na “Hello China” a fadin kasar, a kowacce ranar Laraba daga karfe 5 zuwa 5:30 na yamma.

Shirin ya kunshi koyar da harshen Sinanci da karin haske game da ilimin tattalin arziki da kimiyya da zaman takewa da al’adun kasar Sin. Ana sa ran shirin zai zama wata sabuwar kafa da ‘yan Nijeriya za su samu cikakkiyar fahimta ta ainihin kasar Sin daga bangarori daban daban. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

ACReSAL Ta Kaddamar da Kamfen  Kula Da Sauyin Yanayi A Makarantu

Kungiyar Kano Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes (Kano-ACReSAL) ta kaddamar da yakin neman ilimin sauyin yanayi zuwa Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta ’Yan Mata da ke Kano a wani bangare na shirinta na “Catch Them Young”. Wato Ilmantar da Matasa.

 

Gangamin wayar da kan jama’a wani bangare ne na kashi na biyu na yunkurin aikin na jawo dalibai, malamai, da kwararrun muhalli wajen tattaunawa kan sauyin yanayi da kuma shigar da matasa wajen magance shi.

 

Mukaddashin mai kula da ayyukan, Dr. Abdulhamid Bala, ya sanar da daliban cewa sauyin yanayi ya kasance babban kalubalen da ba za a yi watsi da shi ba.

 

 

“Sauyin yanayi ya kasance barazana mai dorewa ga dorewar duniya. Amsarmu dole ne ta kasance cikin dabaru da gaggawa.”

 

 

Ya bayyana shawarar mayar da hankali kan yaran makaranta. “Muna jan hankalin matasa ta hanyar shirinmu na ‘Catch Them Young’ saboda su ne wakilan canji. Dole ne mu sanya musu kyawawan halaye na muhalli,”

 

 

Dakta Bala ya kuma bukaci dalibai da su taka rawar gani wajen wayar da kan jama’a da tallafawa kokarin kare muhalli.

 

Masana daga Jami’ar Bayero Kano da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kano (KUST) Wudil ne suka jagoranci zaman a lokacin wannan horon nan.

 

Khadija Aliyu/ Kano

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Magance Matsalar Yara Da Ba Sa Zuwa Makaranta: Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyarwa A Makarantun Jihar
  • Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Wata Kungiya Mai Suna “Arewa Cohesion Initiative” Don Maganin Kalubalen Da Yankin Arewa Ke Fuskanta
  • Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
  • ACReSAL Ta Kaddamar da Kamfen  Kula Da Sauyin Yanayi A Makarantu
  • Gamayyar ‘Yan Adawa Sun Kaddamar ADC A Gombe  
  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliyar Kasar Idan Tanaso
  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliya Kasar Idan Tanaso