Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Published: 12th, July 2025 GMT
Ya tunatar da cewa a bara, Antoni-Janar na Ƙasa kuma Ministan Shari’a ya nemi fassarar doka daga Kotun Ƙoli, inda kotun ta tabbatar da cewa kundin tsarin mulki ya tanadi ’yancin cin gashin kai ga ƙananan hukumomi.
“An samu hukunci daga babbar kotun ƙasa da ke nuna cewa kundin tsarin mulkin mu ya tanadi buƙatar ƙananan hukumomi su samu ’yancin kai – su kasance masu cikakken iko da damar aiki a fannoni daban-daban, ko siyasa ko kuma kuɗi,” inji shi.
A cewar sa, bai wa ƙananan hukumomi dama za ta ƙarfafa dimokiraɗiyya a matakin ƙasa da kuma samar da cigaba a cikin al’umma.
Idris ya nuna damuwa kan yadda tsarin ƙananan hukumomi ya raunana a tsawon lokaci, yana nuni da cewa tsarin ya sha bamban da yadda aka tsara shi tun farko.
“Tsawon shekaru, mun shaida yadda ƙarfin ikon ƙananan hukumomi yake ci gaba da raguwa fiye da yadda kundin tsarin mulki ya tanada,” inji shi.
Ya ƙara da cewa Shugaban Ƙasa Tinubu, wanda gwani ne wajen kare dimokiraɗiyya, yana da tabbacin cewa ƙarfafa wannan mataki na gwamnati yana da matuƙar muhimmanci domin cigaban dimokiraɗiyya a ƙasar nan.
“Shugaban Ƙasa ɗan dimokiraɗiyya ne na gaske, kuma yana ganin cewa domin dimokiraɗiyyar mu ta kai inda muke fata, dole ne a ƙarfafa wannan mataki na gwamnati,” inji shi.
Ya buƙaci gwamnoni da su mara wa ƙoƙarin Shugaban Ƙasa baya wajen dawo wa da ƙananan hukumomi ƙarfin su yadda masu tsara kundin tsarin mulki suka nufa tun farko.
Ministan ya kuma gode wa tsofaffin kansilolin bisa jajircewar su wajen kare dimokiraɗiyya, tare da roƙon su da su isar da saƙon gwamnatin Tinubu ga jama’ar ƙasa.
“Ina roƙon ku da ku tallafa wa sauye-sauyen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu. Ba a tsara su domin wahalar da ‘yan Nijeriya ba. E, da farko za su iya kasancewa masu tsauri amma kamar yadda Shugaban Ƙasa ya faɗa, tattalin arzikin mu yana samun daidaito,” inji shi.
Ministan ya bayyana cewa cire tallafin fetur da daidaita farashin musayar kuɗaɗe da aka yi sun haifar da gagarumar riba, wanda hakan ya haifar da ninka kuɗaɗen da ake raba wa jihohi da ƙananan hukumomi domin aiwatar da ayyukan cigaba.
Ya ƙara da cewa kafa kwamitocin cigaba a kowane yanki na ƙasa wani mataki ne na ganin cigaba ya isa kowane lungu da saƙo na Nijeriya.
Tawagar tsofaffin kansilolin ta karrama ministan da Lambar Yabo ta Maida Hankali Kan Jama’a, inda shi kuma ya nuna godiya tare da cewa hakan zai ƙara masa ƙwazo wajen yi wa al’umma hidima.
A nasa jawabin, Sakatare na biyu na ƙungiyar, Mista Cole Michaels, ya yaba da irin yadda ministan yake farfaɗo da hukumomin da ke ƙarƙashin sa domin wayar da kan jama’a kan manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu.
Ya ce an bada lambar yabon ne saboda gudunmawar sa wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya a ƙasar.
Tawagar ta ƙunshi wakilai daga jihohi daban-daban a ƙasar nan, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙungiyar, Mista Auwal Kassim Hassan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Shugaban Ƙasa kundin tsarin
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna
Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa wannan titin ba na yankin Arewa kadai ba ne, ya bayyana shi a matsayin jijiyar ƙasa da ƙasa ne wadda ke haɗa yankuna daban-daban tare da ƙarfafa haɗin kai da bunƙasar tattalin arziki.
Ya kara da cewa titin Abuja- Kaduna da Kano na ɗaya daga cikin manyan ayyukan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ƙarƙashin Manufar Sabon Fata na (Renewed Hope Agenda), wadda ke nufin sabunta manyan gine-ginen ƙasa da inganta tattalin arziki.
Yace “Wannan titi ba hanya ce kawai ba inda yace wata hanya ce ta tattalin arziki wadda ke haɗa mutane, kasuwanni, da dama a fadin Arewacin Nijeriya da ma bayan haka,”
A nasa jawabin, Sanata Umahi ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa yadda yake kaiwa da komowa domin kare muradun al’ummar Kaduna, tare da tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta kuduri aniyar kammala aikin cikin lokaci. Ya bayyana cewa an umarci kamfanonin da ke aikin da su rika aiki sau biyu a rana domin hanzarta cigaba ba tare da rage inganci ba.
Ministan ya kara da cewa amfani da fasahar siminti mai ɗorewa wanda zai tabbatar da cewa titin zai dawwama tare da rage kudin gyara nan gaba.
Kamfanonin da ke aikin sun yi alkawarin ƙara gaggautawa musamman a yankin Jere dake jihar Kaduna, inda ake sa ido sosai kan ci gaban aiki. Gwamnatin Jihar Kaduna ta kuma tabbatar da ci gaba da haɗin kai da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya domin magance ƙalubalen da ke iya janyo tsaiko.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA