Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce umurnin da sojojin Isra’ila suka bai wa Falasɗinawa na ficewa tsakiyar Gaza, babban koma baya ne ga ƙoƙarin ceton rayukan al’ummar yankin da yaƙi ya ɗaiɗaita.

A ranar Lahadi ne Isra’ila ta umarci Falasɗinawa a Deir el-Balah, da su koma kudancin Gaza saboda ayyukan soji.

MDD ta sake nanata gargaɗin da ta yi cewa al’ummar Gaza da dama na mutuwa saboda yunwa kuma suna buƙatar agajin abinci cikin gaggawa yayin da Isra’ila ke ci gaba da taƙaita shigar da kayan agaji.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

Yau Talata, ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai na jerin taruka masu jigon “Kammala shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 14 mai inganci”.

Yayin taron, jami’in kungiyar nakasassu ta Sin ya bayyana cewa, yayin aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 14, an kiyaye hakki da moriyar nakasassu na kasar yadda ya kamata.

A halin yanzu, kasar tana da dokoki da ka’idoji sama da 180 da suka shafi kare nakasassu, ciki har da “Dokar gina muhalli marar shinge”, kuma akwai dokoki da ka’idoji 41 na kasa da suka kara tanade-tanade don kare hakkoki da muradun nakasassu a lokacin tsarawa da gyara abubuwan da suka shafi muhalli.

Bugu da kari, a lokacin aiwatar da “shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 14 mai inganci”, an aiwatar da wani shirin na tsawon shekaru uku (2022-2024) domin taimakawa nakasassu wajen samun ayyukan yi, inda yawan nakasassun dake samun ayyukan yi ya karu akai-akai. Ban da haka kuma, a cikin wannan wa’adi, nakasassu fiye da miliyan 9 ne aka ba su ayyukan yi a fadin kasar, kuma adadin sabbin ayyukan yi na nakasassu a birane da kauyuka ya kai miliyan 2.31. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  •  Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta
  •  Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba
  • Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro
  • Manoma A Kaduna Sun Yabawa Irin Masara Na TELA Saboda Juriyarshi Ga Kwari
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila