Aminiya:
2025-10-15@05:54:50 GMT

Muna tunanin sayar da matatun man Najeriya — NNPCL

Published: 12th, July 2025 GMT

Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL), ya ce ya fara tunanin yiwuwar sayar da matatun man ƙasar nan.

Shugaban kamfanin, Bayo Ojulari ne, ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da Bloomberg.

Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa

Ya ce yanzu haka kamfanin yana sake duba yadda ake gudanar da matatun, kuma ana sa ran kammala wannan nazari kafin ƙarshen shekara.

Da yake magana a taron OPEC karo na tara da aka yi a Birnin Vienna, na ƙasar Austria, Ojulari ya ce gyaran tsofaffin matatun gwamnati ya wuce yadda ake tsammani.

Najeriya na da matatu huɗu; Fatakwal, Warri da Kaduna, amma sun daɗe suna fama da matsaloli kuma ba sa aiki yadda ya kamata.

An daɗe ana kiranye-kiranyen bayar da su ga kamfanonin masu zaman kansu domin kula da su yadda ya kamata.

A watan Nuwamban 2024, NNPCL ta sanar da cewa matatar Fatakwal ta fara tace mai, amma daga bisani aka rufe ta a watan Mayun 2025 saboda matsalolin da suka shafi gyara.

Sauran matatun na Warri da Kaduna har yanzu ana kan gyaran su.

Ojulari ya ce, “Mun kashe kuɗi da yawa kuma mun kawo sabbin dabaru, amma wasu daga cikinsu ba su yi aiki yadda ya kamata.

“Waɗannan matatun tsofaffi ne, kuma suna da wahalar gyaruwa.”

Ya ce yanzu NNPCL na gudanar da cikakken bincike kan tsarin gyaran matatun, kuma sakamakon wannan bincike na iya haifar da sauye-sauye, ciki har da yiwuwar sayar da su.

“Muna fatan kammala binciken nan kafin ƙarshen shekara,” inji shi.

“Sayar da matatun na cikin zaɓin da muke dubawa. Za mu yanke shawara ne bayan mun ga sakamakon wannan bincike.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fatakwal Gyada

এছাড়াও পড়ুন:

Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja

Wani soja mai muƙamin Las Kofur ya ɗirka wa matarsa harbi har lahira sannan ya kashe kansa a Jihar Neja.

Las Kofur Akenleye Femi da ke aiki a Bataliya ta 221, ya yi wannan aika-aika ne a Barikin Sojoji na Wawa da ke Ƙaramar Hukumar Borgu a Jihar Neja.

Muƙaddashin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Soja ta 22 da ke Ilorin, Kyaftin Stephen Nwankwo, ne ya tabbatar da lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce abin ya faru ne a ranar 11 ga Oktoba, 2025.

Ya ce mutuwar sojan da matarsa ta haifar da tashin hankali a cikin sansanin soja, inda mazauna wurin suka shiga ɗimuwa da mamaki kan abin da zai iya jawo irin wannan lamari.

Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako

“An gano gawar Last Kofur Femi da matarsa ne a cikin dakinsu da ke Block 15, Room 24 na Corporals and Below Quarters a Wawa Cantonment,” in ji Kyaftin Nwankwo.

Ya ce binciken farko ya nuna cewa sojan yana kan aiki a cikin sansanin kafin ya nemi izinin zuwa gida domin wasu bukatun kansa, sai daga bisani aka gano gawarsu a gida.

Kyaftin Nwankwo ya ce an ajiye gawar mamatan domin ci gaba da bincike, kuma rundunar sojan na aiki tukuru don gano musabbabin lamarin.

Rundunar Soja ta Najeriya ta bayyana matuƙar baƙin cikinta kan wannan abin takaici, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalai, abokai da abokan aikin mamatan.

Kwamandan Rundunar, Birgediya Janar Ezra Barkins, ya sha alwashin gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar abin da ya faru, tare da ɗaukar matakan da za su hana faruwar irin haka a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali
  • DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?
  • Yadda Najeriya ta casa Jamhuriyar Benin 4-0
  • Ya kamata ‘yan fim su rika taimaka wa kananan cikinsu-Rukayya Abdullahi
  • Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan
  • NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?