Muna tunanin sayar da matatun man Najeriya — NNPCL
Published: 12th, July 2025 GMT
Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL), ya ce ya fara tunanin yiwuwar sayar da matatun man ƙasar nan.
Shugaban kamfanin, Bayo Ojulari ne, ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da Bloomberg.
Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu MusawaYa ce yanzu haka kamfanin yana sake duba yadda ake gudanar da matatun, kuma ana sa ran kammala wannan nazari kafin ƙarshen shekara.
Da yake magana a taron OPEC karo na tara da aka yi a Birnin Vienna, na ƙasar Austria, Ojulari ya ce gyaran tsofaffin matatun gwamnati ya wuce yadda ake tsammani.
Najeriya na da matatu huɗu; Fatakwal, Warri da Kaduna, amma sun daɗe suna fama da matsaloli kuma ba sa aiki yadda ya kamata.
An daɗe ana kiranye-kiranyen bayar da su ga kamfanonin masu zaman kansu domin kula da su yadda ya kamata.
A watan Nuwamban 2024, NNPCL ta sanar da cewa matatar Fatakwal ta fara tace mai, amma daga bisani aka rufe ta a watan Mayun 2025 saboda matsalolin da suka shafi gyara.
Sauran matatun na Warri da Kaduna har yanzu ana kan gyaran su.
Ojulari ya ce, “Mun kashe kuɗi da yawa kuma mun kawo sabbin dabaru, amma wasu daga cikinsu ba su yi aiki yadda ya kamata.
“Waɗannan matatun tsofaffi ne, kuma suna da wahalar gyaruwa.”
Ya ce yanzu NNPCL na gudanar da cikakken bincike kan tsarin gyaran matatun, kuma sakamakon wannan bincike na iya haifar da sauye-sauye, ciki har da yiwuwar sayar da su.
“Muna fatan kammala binciken nan kafin ƙarshen shekara,” inji shi.
“Sayar da matatun na cikin zaɓin da muke dubawa. Za mu yanke shawara ne bayan mun ga sakamakon wannan bincike.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Aref Ya Bayyana Cewa: Iran Ba Ta San Kalmar Mika Wuya Ba A Al’adunta Da Tsaronta
Mataimakin shugaban kasar na farko ya jaddada cewa: Kalmar “mika kai” ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron Iran
Mataimakin shugaban kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya jaddada cewa: kalmar mika wuya ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron kasar.
Arif ya ce: Kamar yadda kuke gani kalmar “mika kai” ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yana mai jaddada cewa, su mutane ne masu wayewa, tare da ingantaccen tarihin al’adu wanda ya wuce dubban shekaru. Ba su neman yaki, kuma ba su fara shi ba. Sun yi imani da zaman lafiya da kwanciyar hankali, kuma a shirye suke don tattaunawa, amma ba za su mika wuya a kowane hali ba.
A wata hira da ya yi da KHAMENEI.IR, Aref ya jaddada cewa: An sha ambaton hakan, sannan kuma Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa ba za mu fara yaki ba, amma idan aka tsokani Iran, to Iran zata mayar da martani, kuma haka yake har yanzu. Maƙiya ‘yan sahayoniyya ba za a taba amince da su ba. An dai tsagaita bude wuta a kasar Labanon, amma kamar yadda ake gani bayan tsagaita wuta an samun adadin shahidai masu yawa. Sadaukarwarsu ta kasance domin kare Iran ce.