NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma
Published: 11th, July 2025 GMT
Dantsoho ya kara da cewa, nuna kwarewar ma’aikata na kara taimaka wa, wajen cimma burin da aka sanya a gaba, musamman a bangaren nuna yin gasa, a tafiyar da Tashohin Jiragen Ruwa.
“Ta irin wannan hanyar ce, za mu iya cimma bukatar da muke da ita da kuma cika muradin masu ruwa da tsaki, da ke a fannin, musamman domin mu kara karfafa karsashin ma’aikatan mu,” Inji Dantsoho.
Dantsoho ya kuma jinjinawa Minsitan ma’aikatar bunsa hada –hadar kasuwanci na kan Teku Adegboyega Oyetola, kan sahalewar Hukumar ta NPA, na yin karin girman ga ma’aikatan da suka amfana, wanda Hukumar ta jima, tana da bukatar yin hakan.
“Dole ne kuma in yabawa Ministanmu Adegboyega Oyetola, kan amincewar da ya yi, na kawo karshen batun yiwa ma’aikatan karin matsayin, ta hanyar gudanar masu da jarrabawar yin gwaji,” A cewar Shugaban.
A na sa jawabin madadin gamayyar kungiyoyin na Tashoshin Jiragen Ruwan kasar SSASCGOC, Kwamarade Bodunde, ya nuna jin dadinsa kan wannan karin matsayin da aka yiwa ma’aikatan.
“Muna kuma godiya, kan inganta walwalar ma’aikatan Hukumar ta NPA da kara inganta ayyukan ‘ya’yan kungiyar, musamman duba da irin yanayin matsin tattalin arzikin da ake fama da ita a kasar, Inji Bodunde.”
Shi kuwa, Janar Manaja a sashen tsare-tsare da samar da bayanai na Hukumar ta NPA Ikechukwu Onyemekara, ya bayyana cewa, zamanantar da kayan aikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, hakan zai kara taimaka wa wajen kara inganta ayyukan ma’aikatan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.
An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.
Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.
An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.
Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.
Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp