Leadership News Hausa:
2025-10-15@05:57:25 GMT

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Published: 11th, July 2025 GMT

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Hukumomin tsaron uku su ne, na DIA, DSS da kuma NIA, inda kuma dokar, ta bayar da damar kafa ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara a fannin tsaro wato ONSA, wadda a baya, ake kiran ofishin da Babban Jami’in Tsaro na Kasa wato CONS.

Wannan Jaridar, na nuna matukar damauwarta kan ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro, da Nijeriya ke fuskata, musamman na rashin gazawar hukumomin tsaro na sirri saboda gasar da suke nuna wa, a tsakaninsu.

A bisa ra’ayinmu, wannan matsalar, abu ne da ke bukatar a kara mayar da hankali cikin gaggawa domin a magance wannan kalubalen na rashin na rashin tsaron.

Sai dai, muna kuma yabawa kokarin da hukumomin tsaron ke ci gaba da yi, na lalubo da mafita kan kalubalen na rashin tsaro.

Amma abin takaici ne, kan yadda gasar a tsakanin hukumomin tsaron kasar, ke kara haifar da kalubalen na rashin tsaro wanda kamata ya yi ace, suna yin aiki tare, domin a samar wa da ‘yan Nijeriya sauki, wajen magance masu kalubalen rashin tsaron, da suke ci gaba da fuskanta.

Hatta shi ma tsohon Babban Hafsan Tasron kasar ya tabbatar da cewa, akwai bukatar hukumomin tsaro na sirri na kasar, su kara zagaewa wajen samar da dabarun kara ciyar da hukumomin na tsaro.

Wasu kwararru na ganin cewa, akwai bukatar hukumomin tsaron su hada kai domin samar da tsaro a kasar.

Gasar da ke ci gaba da aukuwa a tsakanin hukomomin tsaron su kasance suna samar da bayanan sirri a tsakaninsu, domin a dakile kalubalen rashin tsaro a kasar.

Masu ruwa da tsaki a kasar, ciki har da shugaba Bola Ahmed Tinubu, na ci gaba da nuna damuwarsu, kan kalubalen rashin tsaro a kasar, musamman duba da yadda Tinubu, a wani taro na kwanan baya ya sanar da cewa, kalubalen rashin tsaro a karni na 21, abu ne da ake bukatar hada kai, amma ba wai batun nuna yin gasa, a tsakanin hukumomin tsaron kasar ba.

Kalubalen ta’addanci a Arewa Maso Gabas, matsalar ayyukan ‘yan bindiga a Arewa Maso Yamma, fashi a Tekunan ruwa a Tekun Guinea, rikicin manoma da makiyaya a yankin Middle-Belt, batun ‘yan aware a yankin Kudu Maso Gabas, wadannan matsalolin, abu ne, da yafi karfin hukumar tsaro daya, ta kawo karshensu.

Kazalika, hare-haren da suka janoyo kashe wasu kauyawa kimanin su 200 a daren ranar 13 na watan Yunin 2025 yankin Yelwata, na karamar hukumar Guma a jihar Biniwe da kuma sake dawor ayyukan ‘yan ta’addar Boko Haram a yankin Arewa Maso Gabas, hakan ya nuna a zahiri, akwai bukatar hukumomin tsaron su hada kai domin tunkarar kalubalen na rashin tsaro da kuma kawo karshen sa, musamman duba da cewa, matsalar na kara zama barazana ga tattalin arzikin.

Sai dai, hakan ya nuna cewa, kusan babu wani katabus da hukumomin tsaron ke yi, na magance kalubalen na rashin tsaron.

A ra’ayin wannan Jaridar, akwai matukar bukatar Gwamnati ta dauki kwararan matakai, musamman domin gano ainahin tushen matsalar ta rashin tsaro, da kuma magance ta.

Sai dai, wani kokari daya shi ne, na kara fadada mahukuntan na tsaron sirri wato kafa cibiyar kasa ta dakile yunkurin ayyukan ta’addanci NCTC.

Bukatar hukumomin tsaron na sirri, na yin aiki a tare, abu ne da yake da matukar mahimmanci, musamman domin a magance kalubalen rashin tsaro, da Nijeriya ke fusanta.

Ra’ayin wannan Jaridar shi ne, akwai bukatar hukumomin tsaro na sirri na kasar, su jingine batun gasa a tsakaninsu, su mayar da hankali, wajen lalubo da mafita, kan kalubalen rashin tsaro a kasar.

Kazalika, duba da irin yanayin na barazar rashin tsaron, ya kamata a kara zuba kudade wajen kara darajar kayan kimiyya na aikin tsaro na hukumomin tsaron kasar, wanda hakan zai kara masu kwarin guiwar, kara mayar da hankali a ayyukansu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro Nijeriya akwai bukatar hukumomin tsaro kalubalen na rashin tsaro kalubalen rashin tsaro a hukumomin tsaron rashin tsaron tsaro a kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh

Shugaban kasar Amurka Donal trump da shugaban kasar Masar Abdulfatta Assisi ne zasu jagoranci bikin rattaba hannu kann yarjeniyar Sulhu wacce ta kawo karshen yaki da kuma kissan kiyashin da HKI ta yi a Gaza na tsawon shekaru 2, daga ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 zuwa ranar Alhamis 8 ga watan Octoban shekara ta 2025.

Shafin yanar gizo na labarai ArabNews ya bayyana cewa babban sakataren MDD Antonio Gutteres da shuwagabanin kungiyoyin kasashen Larabawa da Turai zasu halittu taron na gobe litinin a sharam Sheikh na kasar Masar.

Labarin ya kara da cewa za’a gudanar da taron ne a gobe litinin, bayan azahar kuma ana saran shuwagabannin kasashe fiye da 20.

Firai ministan kasar Burtaniya Keir Starmer, na Italiya,  Giorgia Meloni da kuma  Pedro Sanchez firai ministan kasar Spain. Da kuma shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron zai sami halattan taron.

Labarin ya kamala da cewa babu tabbas kan cewa Benyamin Natanyahu Firai ministan HKI zai halarci taron saboda yadda wasu shuwagabannin da suke halattan taron suke kinsa. Hossam Badran na kungiyar Hamas yace reshen kungiyar Hamas bata cikin yarjeniyar. Za’a fara aiwatar da musayar Fursinoni a gobe litinin tsakanin bangarorin biyu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100% October 12, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha October 12, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga ‘Yar Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
  • Cibiyar Lafiya Ta Nasser Ta Ce: Yaran Gaza 5,500 Suna Bukatar Agajin Gaggawa A Kasashen Waje
  • Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”
  • Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
  • An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
  • Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh
  • An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan