Ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon ta yi furuci da cewa hakika an lalata sansanin sojin saman Amurka na Al Udeid na Qatar

Kakakin ma’aikatar tsaron Amurka Sean Parnell ya yi furuci da cewa: Makami mai linzami na Iran da aka kai hari da shi kan sansanin jiragen sama na Al Udeid da ke Qatar, a harin da Iran ta kai a watan Yunin da ya gabata ya janyo barna.

Sanarwar ta Pentagon ta zo ne bayan da Kamfanin Dillancin Labarai na Associated Press ya wallafa hotunan tauraron dan adam da ke nuna irin barnar da harin ya janyo wanda shugaban Amurka Donald Trump ya musanta a lokacin.

A cewar hotunan tauraron dan adam da kamfanin dillacin labarai na Associated Press ya yi nazari a ranar Juma’a, harin da Iran ta kai kan sansanin Al Udeid da ke Qatar ya yi kamari kuma ya afkawa wani gida mai dauke da kubba mai kusurwa uku da Amurkawa ke amfani da su wajen samun amintattun hanyoyin sadarwa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

  Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i Kadan

Ma’aikatar kiwon Lafiya ta Falasdinawa ta sanar a jiya Juma’a cewa; An kai gawawwakin shahidai 61 zuwa asibitocin yankin Gaza, a cikin sa’oi 24.

Ya zuwa yanzu adadin mutanen Gaza da su ka yi shahada tun daga 2023 sun kai 57,823, sai kuma wadanda su ka jikkata da sun kai 137,887.

Su kuwa Falasdinawan da sojojin HKI su ka kashe a wurin karbar kayan agaji sun kai 788, sai kuma wasu 5,199 da su ka jikkata.

Ma’aikatar kiwon lafiyar ta Falasdinawa ta kuma bayyana cewa da akwai wasu dubban Falasinawa shahidai da suke kwance a karkashin baraguzai, kuma rashin kayan aiki ba zai sa a isa inda suke ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; An Mika Batun Hakin Gwiwa Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA Ga Kwamitin Kolin Tsaron Kasa
  •   Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i Kadan
  • Associated Press: Harin Iran Akan Sansanin Amurka Dake Kasar Qatar Ya Lalata Wata Cibiyar Sadarwa
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah  Wadai Da Kakaba Takunkumi Kan Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya
  • Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara
  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana
  • An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba
  • Somaliya: Kungiyar Al-Shabab Ta Kai Wa Barikin Soja Hari A Birnin Magadishu
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana cewa: Martanin Da Iran Ta Mayar Ne Ya Sanya Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta