HausaTv:
2025-09-17@22:31:38 GMT

Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran

Published: 23rd, July 2025 GMT

Kasashen Iran, Rasha, da China sun gudanar da wani taro a birnin Tehran, inda suka tattauna batutuwan da suka shafi Shirin Iran na nukiliya da kuma dage takunkumin da aka kakaba mata.

Taron kasashen ya tabbatar da aniyarsu ta ci gaba da yin hadin gwiwa da tuntubar juna a cikin lokuta masu zuwa.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya bayar da rahoton cewa, a wannan Talata 22 ga watan Yuli 2025, aka gudanar da taron tawagogin kasashen uku.

Mahalarta taron a karkashin inuwar ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran, sun tabbatar da aniyar kasashensu na ci gaba da yin hadin gwiwa tare da yin musayar ra’ayi kan batutuwan da suka shafi yarjejeniyar nukiliyar.

Sun kuma jaddada muhimmancin ci gaba da wannan shawarwari domin biyan muradun kasashen uku wajen tinkarar manufofin kasashen yamma, musamman takunkuman Amurka.

Tawagogin sun amince su ci gaba da bude hanyoyin karfafa alakokinsu da kuma ci gaba da gudanar da taruka a nan gaba a matakai daban-daban a cikin makonni masu zuwa, a wani bangare na abin da suka bayyana da “kokarin hadin gwiwa na tallafawa zaman lafiyar yankin da inganta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai

Rikicin kwamitin gudanarwa da malaman Kwalejin Fasaha ta Tarayya da ke Bida (Bida Poly), ya ƙara ƙamari bayan da makarantar ta dakatar da ayyukan Kungiyar Malamai (ASUP) sannan ta kawo sojoji domin kula da jarrabawa da dalibai ke gudanarwa.

Ƙungiyar ASUP reshen kwalejin ta shiga yajin aiki mara wa’adi, domin neman a biya su alawus ɗin ƙarin aiki na watanni 18 da suka wuce.

Ƙungiyar ta umarci mambobinsu da kada su gudanar da jarrabawar zangon da ta fara ranar Litinin, 15 ga Satumba, 2025.

Wani ma’aikacin makarantar ya shaida wa wakilinmu cewa sojojin an gayyace su ne domin kare ɗalibai da wasu malamai daga shirin da ASUP ke yi na hana gudanar da jarrabawa.

’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu An kama su kan satar zinarin Naira miliyan 110 a Kebbi

“Ba wai don su gudanar da jarrabawar aka kawo sojojin ba, sai don su kare ɗalibai da malamai daga duk wani cikas. Amma abin mamaki shi ne, me ya sa aka kawo sojoji maimakon ’yan sanda ko Sibil Difens?” in ji shi.

Shugaban ASUP na kwalejin, Kwamared Kolo Joshua, ya tabbatar da komawar su yajin aiki, yana mai cewa gwamnati ta yi biris da haƙƙoƙin malaman.

“Shekaru biyu ke nan muna jurewa, amma yau malaman suna bin bashin watanni 18 na kuɗin ƙarin aiki.

“Duk da tattaunawa da saƙonni da muka aika, ba a ɗauki mataki ba. Sai ma aka dakatar da ƙungiya sannan aka fara tsoratar da shugabanninmu da tambayoyi. Wannan ya jefa malaman cikin rashin kuɗi da raguwar ƙwarin guiwa,” in ji shi.

Ya ce sai dai idan gwamnati ta biya hakkokin malamai da kuma ta koma kan tattaunawa ta gaskiya ne za a samu zaman lafiya a makarantar.

Wata sanarwa da Babban Sakataren Makarantar, Hussaini Mutammad Enagi, ya fitar, ta ce an dakatar da ayyukan ƙungiyar ne bisa dalilin “fargba da kuma rahoton tsaro mai tayar da hankali.”

Sai dai jami’in hulɗa da jama’a na makarantar, Malam Abubakar Dzukogi, ya musanta cewa sojoji aka kawo.

“Na zagaya duk cibiyoyin jarrabawa, ban ga sojoji ba. ASUP ne kawai suka shiga yajin aiki, sai makaranta ta ci gaba da gudanar da jarrabawar. Wannan lamari na farar hula ne, ba na soja ba,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
  • Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Runduwar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar