Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ya bukaci Isra’ila ta saki wani ma’aikacin hukumar da ya ce sojojin Isra’ila sun kama a wani farmaki da suka kai a tsakiyar Gaza ranar Litinin.

Tedros Ghebreyesus ya ce sojojin sun jefa ma’aikatan agaji da iyalansu cikin hatsari a lokacin da suka shiga gidajensu da kuma babban dakin ajiyar kaya a Deir al-Balah.

Ya yi alƘawarin cewa WHO za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta a yankin.

Deir al-Balah dai na cike makil da Falasɗinawa da suka rasa matsugunansu a kusan shekaru biyu na yakin Gaza

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Birgediya Janar Sabahi Fard Ya Jaddada Cewa: Duk Wani Sabon Hari Kan Iran Zai Fuskanci Martani Mai Gauni

Kwamandan rundunar hadin gwiwar hedikwatar tsaron saman Iran ya jaddada cewa: Duk wani sabon kuskure da ‘yan sahayoniyya suka aikata zai haifar da mummunan sakamako

Kwamandan rundunar hadin gwiwar hedikwatar tsaron saman Iran kuma  kwamandan bataliyar Khatam al-Anbiya (s.a.w) Birgediya Janar Alireza Sabahi Fard, ya jaddada cewa: Duk wani sabon kuskure da yahudawan sahayoniyya za su sake yi, zai haifar da mummunan sakamako.

Birgediya Janar Seyyed Majid Mousavi, kwamandan rundunar sararin samaniyar Iran na dakarun kare juyin juya halin Musulunci ta Iran ya ziyarci hedikwatar hadakar tsaron sojojin saman na Khatam al-Anbiya, inda ya tattauna da Birgediya Janar Sabahi Fard, kan sakamakon arangamar da sojoji suka yi a baya-bayan nan da kuma hanyoyin inganta hadin kan tsaro.

A zaman taron, Sabahi Fard ya ce, “Tsarin tsaron saman kasar Iran ya shiga cikin yakin kwanaki 12 na baya-bayan nan da jajircewa da himma, tare da yin nasara ta hanyar hadin gwiwa da daukar matakin jihadi wajen dakile manufofin makiya yahudawan sahayoniyya tare da tilasta musu ja da baya. Ya bayyana karara cewa ci gaba da ta’addancin yana kara ta’azzara halin da ake ciki a cikin yankunan da aka mamaye, musamman a Tel Aviv da Haifa.”

Ya kara da cewa, “Suna dogara da karfin kasa wajen bunkasa na’urar tsaronsu, kuma jinin shahidansu ko daga sojoji ne ko farar hula, ba zai zuba a banza ba. Zai haifar da mummunan tasiri kan ‘yan mamayar yahudawan sahayoniyya. Kisan gillar da aka yi wa masana kimiyyar nukiliya da shugabannin tsaron Iran ba zai hana kasar cimma nasarorin fasaha, soja, da tsaro ba. Maimakon haka, za su yi aiki a matsayin wani gagarumin shiri na yaki da makiya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  •  Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta
  •  Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba
  • Yunwa na ƙara tsanani a Arewa maso Gabashin Nijeriya — ICRC
  • An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano
  • MDD Ta Gargaɗi Isra’ila Kan Tilasta Wa Al’ummar Deir al-Balah Na Gaza Tashi
  • Birgediya Janar Sabahi Fard Ya Jaddada Cewa: Duk Wani Sabon Hari Kan Iran Zai Fuskanci Martani Mai Gauni
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi