Isra’ila Ta Kashe Kananan Yara Masu Dibar Ruwa A Gaza
Published: 13th, July 2025 GMT
Hukumar bayar da agajin gaggawa a Gaza ta ce aƙalla mutum 10, ciki har da ƙananan yara guda shida ne suka rasu a sanadiyar harin da Isra’ila ta kai ta sama a Gaza a safiyar Lahadi.
An kai gawarwakin waɗanda suka rasu zuwa asibitin Nuseirat’s al-Awda, inda wani likita ya ƙara da cewa sun yi jinyar wasu mutum 16, ciki har da ƙananan yara guda bakwai.
Wani ganau ya ce jirgi mara matuƙi ne ya harba makami mai linzami a kan dandazon mutanen da suka yi layi riƙe da jarkunansu domin ɗibar ruwa daga wata tankar ruwa a sansanin ƴangudun hijira na al-Nuseirat.
Har zuwa haɗa wannan rahoton, rundunar tsaron Isra’ila ba ta ce komai ba kan batun.
Wani faifan bidiyo da BBC ba ta tantance ba ya nuna ƙananan yara jina-jina, da gawarwakin wasu, wasu kuma suna ta ihu, sannan wasu suka zo daga bisani suna kwashe mutanen zuwa asibiti a motoci da amalanke.
Isra’ila ta fara kai hare-hare ne a Gaza tun bayan harin Hamas a ƙasar a ranar 7 ga Oktoban 2023, inda ƴan Hamas ɗin suka kashe 1,200, sannan suka yi garkuwa da wasu 251.
Zuwa yanzu Isra’ila ta kashe aƙalla mutum 57,882 a Gaza, kamar yadda ma’aikatar lafiyar yanki ta bayyana.
Haka kuma an tarwatsa sama da kashi 90 na gidajen zirin, sannan an lalata asibitoci da cibiyoyin ruwan sha da sauran abubuwan more rayuwa, wanda hakan ye jefa yankin cikin ƙarancin abinci da magani da man fetur.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
Babbar Kotun Kano mai lamba 7 da ke zama a cikin birni ta bayar da umarnin tsare Aminu Ismail, mazaunin Unguwar Bai a Karamar Hukumar Ajingi ta jihar, bisa zarginsa da kashe mahaifinsa, Malam Dahiru Ahmad, ta hanyar caka masa wuƙa har lahira.
Lamarin ya faru ne bayan samun sabani tsakaninsu kan aniyar Aminu ta ƙara aure, wadda mahaifinsa ya ƙi goyon baya saboda abin da ya kira halin tattalin arzikin da ake fama da shi a kasa.
Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – ZulumA cewar lauyan masu ƙara, Barrista Lamido Abba Sorondinki, wanda ake tuhuma ya shaida wa mahaifinsa niyyarsa ta kara mata ta biyu, amma mahaifinsa ya ba shi shawarar kada ya yi hakan, yana mai danganta matsalar da halin tattalin arzikin ƙasa ke ciki.
Wannan sabani ya rikide zuwa faɗa, inda ake zargin Aminu da caccaka wa mahaifin nasa wuƙa a ƙirji, lamarin da ya jawo masa rauni mai tsanani har ya rasa ransa.
An gurfanar da Aminu da laifin kisan kai, wanda ya saba da Sashe na 221 na kundin penal code.
Ana ci gaba da shari’ar, kuma kotu ta bayar da umarnin tsare shi har zuwa lokacin da za a ci gaba da sauraron ƙarar.