Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-17@22:28:56 GMT

Isra’ila Ta Kashe Kananan Yara Masu Dibar Ruwa A Gaza

Published: 13th, July 2025 GMT

Isra’ila Ta Kashe Kananan Yara Masu Dibar Ruwa A Gaza

Hukumar bayar da agajin gaggawa a Gaza ta ce aƙalla mutum 10, ciki har da ƙananan yara guda shida ne suka rasu a sanadiyar harin da Isra’ila ta kai ta sama a Gaza a safiyar Lahadi.

An kai gawarwakin waɗanda suka rasu zuwa asibitin Nuseirat’s al-Awda, inda wani likita ya ƙara da cewa sun yi jinyar wasu mutum 16, ciki har da ƙananan yara guda bakwai.

Wani ganau ya ce jirgi mara matuƙi ne ya harba makami mai linzami a kan dandazon mutanen da suka yi layi riƙe da jarkunansu domin ɗibar ruwa daga wata tankar ruwa a sansanin ƴangudun hijira na al-Nuseirat.

Har zuwa haɗa wannan rahoton, rundunar tsaron Isra’ila ba ta ce komai ba kan batun.

Wani faifan bidiyo da BBC ba ta tantance ba ya nuna ƙananan yara jina-jina, da gawarwakin wasu, wasu kuma suna ta ihu, sannan wasu suka zo daga bisani suna kwashe mutanen zuwa asibiti a motoci da amalanke.

Isra’ila ta fara kai hare-hare ne a Gaza tun bayan harin Hamas a ƙasar a ranar 7 ga Oktoban 2023, inda ƴan Hamas ɗin suka kashe 1,200, sannan suka yi garkuwa da wasu 251.

Zuwa yanzu Isra’ila ta kashe aƙalla mutum 57,882 a Gaza, kamar yadda ma’aikatar lafiyar yanki ta bayyana.

Haka kuma an tarwatsa sama da kashi 90 na gidajen zirin, sannan an lalata asibitoci da cibiyoyin ruwan sha da sauran abubuwan more rayuwa, wanda hakan ye jefa yankin cikin ƙarancin abinci da magani da man fetur.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta

Kungyar Hamas ta bayyana cewa: Gmanatin mamayar Isra’ila ta ƙirƙiri ƙarya don kare kisan gillar da ta yi a Gaza

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta tabbatar da cewa: Zargin da kakakin rundunar sojin mamayar Isra’ila ya gabatar dangane da yin amfani da hasumiyai a birnin Gaza domin aikin soji ba komai ba ne illa karairayi na zahiri da suke nufin kare laifukan da ake aikatawa da kuma boye barnar da ake yi a birnin Gaza, kamar yadda a baya sojojin mamaya suka lalata garuruwan Rafah, Khan Younis, Jabaliya, Beit Hanoun, da Beit Lahiya.

A cikin wata sanarwa da kungiyar Hamas ta fitar ta bayyana cewa, zargin mamaya na cewa kungiyar Hamas na amfani da fararen hula a matsayin garkuwar dan adam tare da hana su ficewa daga Gaza, yaudara ce karara da ke nuna rashin mutunta ra’ayin al’ummar kasa da kasa tare da tabbatar da dagewar da take yi na ci gaba da kisan kiyashi kan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba da kuma raba su da muhallinsu da karfi da nufin korar su daga zirin Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha September 17, 2025 Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta
  • Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa