Leadership News Hausa:
2025-10-15@19:02:07 GMT

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

Published: 11th, July 2025 GMT

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

Amurka ta bayyana dalilin sabunta manufofin, tare da lura da cewa “an tsara sharuddan bizar Amurka da ka’idoji domin kare tsarin shige da fice na Amurka.”

Ofishin jakadancin ya kara da cewa “wadannan ka’idoji sun dogara ne kan ma’aunin fasaha da tsaro na duniya.”

A cewar ofishin jakadancin Amurka yana aiki tare da hukumomin Nijeriya domin cimma wadannan matakan.

Sanarwar ta ce “Tawagar Amurka tana aiki tare da gwamnatin Nijeriya domin tabbatar da cewa Nijeriya za ta iya cika sharuddan.”

Misalin wannan sabon tsari ya hada da “Takardun tafiye-tafiye masu aminci: tabbatar da cewa kasashe suna ba da amintattun takaddun balaguro tare da ingantattun bayanan matafiyi, Kada aikin gudanar da Bisa ya wuce lokacin da aka dauka:.”

Duk da sabbin takunkumin, ofishin jakadancin ya sake jaddada alakar diflomasiyya da Nijeriya.

Sanarwar ta kara da cewa, “Amurka na mutunta dangantakarta da Nijeriya da dadewa, kuma tana ci gaba da jajircewa wajen fadada hadin gwiwarmu bisa mutunta juna, da muhimman batutuwan tsaro, da damar tattalin arziki, tare da tabbatar da tsaron kasashen biyu.”

Har ila yau, ofishin jakadancin ya nuna goyon bayansa ga sauye-sauyen da Nijeriya ke ci gaba da yi, inda ta ce, “Mun yaba da kokarin da hukumomin shige da fice da na tsaro na gwamnatin Nijeriya ke yi na ganin sun cika ka’idoji kyawawan ayyuka na kasa da kasa.”

An shawarci matafiya na Nijeriya da su bi ka’idojin bizar.

“An bukaci matafiya ‘yan Nijeriya da su mutunta tare da kiyaye sharuddan bizarsu, kuma su tabbatar da ingantattun takaddun balaguro, kuma na zamani.”

Ofishin jakadancin ya karkare da jaddada huldarsa da jama’a da gwamnatin Nijeriya.

“Amurka ta kasance amintacciya a cikin zurfafa dangantakar jama’a da Nijeriya ta hanyar kasuwanci, ilimi da mu’amalar al’adu.

“Muna fatan ci gaba da hadin gwiwa a dukkan matakai tare da jama’ar Nijeriya da jami’an gwamnati don tabbatar da tafiya cikin aminci da doka tsakanin Amurka da dukkan kasashe,” in ji ta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jakadancin ya da Nijeriya tabbatar da Nijeriya da

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Tsohon Gwamnan Jihar Ribas ya yi gargaɗin cewa dogaro da soja kaɗai, ba tare da inganta rayuwar jama’a ba, zai ƙara haifar da rikice-rikice.

Ya ƙara da cewa ingantacce  tsaro na ƙasa yana farawa ne idan gwamnati ta ƙirƙiro damarmakin samun aiki da kuma mayar da amincin jama’a ga gwamnati.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa October 14, 2025 Manyan Labarai Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan October 14, 2025 Manyan Labarai Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026 October 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
  • Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe
  • Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu
  • An Bukaci An Bukaci Asusun JICHIMA Ya Fadada Hanyoyin Samun Kudade Baya Ga Gwamnatin Jigawa
  • Jihar Kano Na Aikin Gyaran Cibiyoyin Lafiya Da Za Su Yi Gogayya Da Na Ƙasashen Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano