Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-03@07:58:29 GMT

Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano

Published: 22nd, July 2025 GMT

Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano

Mazauna unguwar Zangon Kaya da ke karamar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano sun shiga cikin makoki sakamakon nutsewar da wasu matasa hudu suka yi a hanyar ruwa da baraguzan gine-gine suka tushe.

 

Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Yusif, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin.

 

A cewarsa, lamarin ya faru ne bayan wadanda lamarin ya rutsa da su suka shiga mashigar ruwa da suka taru sakamakon toshewar hanyar jirgin da ake yi.

 

Ya kara da cewa, kamar yadda shaidun gani da ido suka bayyana, da farko biyu daga cikin wadanda abin ya shafa sun shiga cikin ruwan da nufin yin iyo amma sun makale. A kokarin ceto su, mutum na uku ya shiga, shi ma ya makale. Abin baƙin ciki, mutum na huɗu, yana ƙoƙari ya ceci sauran, ya fuskanci irin wannan matsalar.

 

Saminu ya yi nuni da cewa, kafin isowar hukumar kashe gobara mazauna yankin sun yi nasarar ceto biyu daga cikin wadanda abin ya shafa. Yayinda “Sauran biyun, tawagar ceto ta fito da

 

Wadanda abin ya shafa sun hada da Nasirudden Tasi’u dan shekara 25 da Basir Sani mai shekaru 28 da Yakubu Muhd dan shekara 22 da Usman Ubale dan shekara 26.

 

Jami’in hulda da jama’a ya yi nuni da cewa, an samu dukkanin mutane hudun a sume kuma daga baya aka tabbatar da sun mutu.

 

“An mika gawar su ga SP Abdulkadir M. Albasu na sashin ‘yan sanda na Dawanau domin ci gaba da bincike”.

 

Saminu ya ce, Daraktan hukumar kashe gobara ta jiha Alhaji Sani Anas ya jajantawa iyalan mamatan.

 

Ya kuma gargadi jama’a da su guji shiga cikin ruwa ba tare da izini ba ko kuma masu hadari, musamman wadanda ayyukan gine-gine ya shafa.

 

“Muna kira ga ‘yan ƙasa da su guji yin iyo ko wasa a cikin kududdufi, musamman waɗanda aka toshe ko ba a tsara su don amfani da nishaɗi ba.

 

Al’umma na ci gaba da nuna alhininsu yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kan al’amuran da suka dabaibaye wannan mummunan lamari.

 

Rel/Khadijah Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

Gwamna Inuwa ya kuma jaddada bukatar bin ka’idojin kariya a harkokin sufurin ruwa, inda ya yi kira ga shugabannin kananan hukumomi, da shugabannin al’umma, da direbobin kwale-kwale da hukumomin da ke da ruwa da tsaki da sauran wadanda suka dace su kara kaimi wajen ganin ana kiyaye duk ka’idojin kariya don magance sake afkuwar ibtila’in a nan gaba.

Ya umurci Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA) da Majalisar. Karamar Hukumar Nafada su bayar da duk wani tallafin da ya dace ga iyalan da abin ya shafa tare da hada hannu da hukumomin da abin ya shafa don inganta tsaro da wayar da kan al’ummomin da ke yankunan kogi.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi addu’a yana mai cewa “A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, ina mika sakon ta’aziyyarmu ga iyalan mamatan tare da addu’ar Allah ya jikansu da rahama ya gafarta musu kurakuransu, ya kuma saka musu da Aljannar Firdaus”.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025 Manyan Labarai Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi October 31, 2025 Manyan Labarai Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi