Jihar Kano Za Ta Hada Gwiwa FMBN Don Samar Da Gidaje Masu Saukin Kudi
Published: 24th, July 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana aniyarta na ci gaba da hadin gwiwa da Bankin Lamunin Gidaje na Tarayya (Federal Mortgage Bank of Nigeria – FMBN) domin shawo kan matsalar karancin gidaje a jihar.
Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana hakan yayin wata ganawa da Babban Daraktan bankin Alhaji Shehu Usman Osidi a ofishinsa.
Gwamna Yusuf ya bayyana muhimmancin wannan hadin gwiwa, yana mai jaddada Kano a matsayin jiha ta biyu mafi yawan jama’a a Najeriya, inda adadin mutanenta ke kara karuwa cikin sauri.
“Kano tana daga sahun gaba wajen ci gaba, kuma samar da gidaje na daga cikin muhimman ginshikai na wannan ci gaba. Akwai bukatar samar da gidaje masu araha domin inganta rayuwar jama’a.” In ji Gwamnan.
A nasa bangaren, Alhaji Shehu Usman Osidi, Manajan Darakta na FMBN, ya bayyana manufar bankin a matsayin taimaka wa ‘yan Najeriya, musamman masu karamin karfi da matsakaicin albashi, wajen samun gidaje masu inganci da saukin kudi.
Ya yabawa gwamnatin Jihar Kano bisa dawo da kanta cikin tsarin Asusun Kasa na Gidaje (National Housing Fund – NHF), yana mai bayyana hakan a matsayin shaida ta shugabanci nagari da jajircewar inganta jin dadin ma’aikata.
Osidi ya bayyana cewa FMBN na da wasu ayyukan rukunin gidaje guda 10 a Kano da suka kai kimanin Naira biliyan 6.8, da nufin rage gibin gidaje da ake fuskanta a jihar.
Ya kuma bayyana shirye-shiryen bankin na kara zurfafa hadin gwiwa da gwamnatin Kano domin cimma burinsu na bai daya.
“Jihar Kano ta koma tsarin NHF a watan Janairun 2025, bayan janyewa tun shekarar 2002. Wannan hadin gwiwa zai taimaka wajen samar da mafita ta gidaje ga ma’aikata tare da inganta walwalarsu,” inji Osidi.
Daga Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: hadin gwiwa
এছাড়াও পড়ুন:
Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
Da yake kaddamar da shirin, Darakta Janar na IRM, Alhaji Anas Muhammad, ya ce an kirkiro da shirin ne domin karfafa zaman lafiya da hadin kai ta hanyar tallafa wa Musulmai da Kiristoci ta bangaren samar da kiwon lafiya da bayar da tallafin kayan abinci da jari.
Ya ce: “Kalubalen lafiya ba sa bambance addini ko kabila, don haka bama bambantawa wajen bayar da tallafin. in sha Allah zamu ci gaba da aiwatar da irin wannan shiri a fadin jihar Kaduna baki daya.”
A nasa jawabin, Shugaban hukumar KADCHMA, Malam Abubakar Hassan, ya bayyana cewa wannan hadin gwiwa tana nuna muhimmancin dangantaka tsakanin gwamnati da kungiyoyi masu zaman kansu wajen cimma dorewar tsarin inshorar lafiya ga kowa.
Ya kara da cewa kaddamar da inshorar lafiya kyauta na shekara guda babban ci gaba ne a cikin gyaran fannin lafiya da ake gudanarwa a jihar, inda ya yaba da kokarin gidauniyar IRM wajen tallafawa rayuwar al’ummar Kaduna – Musulmai da Kiristoci.
Wasu daga cikin wadanda suka amfana da shirin daga Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) reshen Kaduna da kuma kungiyar ci gaba ta Darikar Tijjaniyya ta jihar Kaduna sun bayyana farin ciki da godiya ga gidauniyar da kuma gwamnatin jihar, inda suka ce inshorar lafiya kyauta za ta rage musu nauyin kashe kudin magani tare da karfafa hadin kai a tsakanin al’umma da samar da zaman lafiya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA