Tinubu ya sake miƙa buƙatar karɓo bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare
Published: 24th, July 2025 GMT
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya miƙa wa Majalisar Dokokin Tarayya buƙatar ƙara ranto bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare, ƙarƙashin shirin ciyo bashin na gwamnatin tarayyar na 2025 zuwa 2026.
Hakan na ƙunshe cikin wata takarda da Tinubu ya aikewa majalisar, wadda Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas ya karanto a zamansu na yau Laraba.
Takartar ta ambato shugaban ƙasar na cewa karɓar rancen ya zama tilas saboda buƙatar ƙarin kuɗi da aka yi a aikin babbar hanyar Lagos zuwa Calabar, wanda ya tashi daga Dala miliyan 700 zuwa Dala miliyan 747 — ƙarin Dala miliyan 47 ke nan.
Idan ba a manta ba, a jiya Talata ne Majalisar Datttawan Nijeriya ta sahale wa shugaba Tinubu karɓo bashin Dala biliyan 21 daga ƙetare domin cike giɓin kasafin kuɗin kasar na bana zuwa baɗi.
Ko a watan Nuwambar 2023, majalisar wakilai da ta dattawa sun amince da ciyo bashin Dala biliyan 7 da miliyan 800, da kuma Euro miliyan 100 domin gudanar da manyan ayyuka da sauran ayyukan raya ƙasa.
Kazalika, a watan Maris ɗin 2025 ma majalisar ta amince Tinubu ya ciyo bashin Dala biliyan 21 da miliyan 500 daga ƙetare, da kuma karɓar takardun kuɗin banki da suka kai Naira biliyan 757 da miliyan 900 domin biyan ‘yan fansho haƙƙoƙinsu.
Ya zuwa watan Maris dai, adadin bashin da ake bin Najeriya ya kai Dala biliyan 91 kwatankwacin Naira tiriliyan 121, a cewar wani rahoton ofishin kula da basuka na ƙasar DMO.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai rance Dala miliyan daga ƙetare Dala biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Cikin jadawalin GII na 2025, kasashe masu karanci da matsakaicin kudin shiga 17, sun taka rawar gani fiye da yadda aka yi hasashe, bisa matsayin ci gabansu, yayin da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara ke kan gaba, cikin kasashe mafiya samun ci gaban kirkire-kirkire, inda kasashen Afirka ta Kudu, da Senegal da Rwanda ke kan gaba a jerin kasashen shiyyar. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp