Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya gabatar da matsayar  Jihar Kaduna a zaman jin ra’ayin jama’a dangane da gyaran kundin tsarin mulkin shekarar 1999.

An gudanar da taron ne a gidan Gwamnati na General Hassan Katsina da ke Kawo, a garin Kaduna, a matsayin wani bangare na ci gaba da shirin gyaran kundin tsarin mulki da Majalisar Wakilai ta kasa ke jagoranta.

Wannan zaman jin ra’ayi da aka ware a matsayin Cibiyar ta daya, ya hada da jihohin Kaduna, Kano, Katsina da Jigawa.

Taron ya tara shugabanni daga fannoni daban-daban ciki har da ’yan siyasa, da sarakuna da kuma wakilan kungiyoyin fararen hula, domin tattauna batutuwan da suka shafi sauye-sauyen kundin tsarin mulki.

Cikin manyan bakin da suka halarci taron sun hada da Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Dr. Hadiza Balarabe, wacce ta wakilci Gwamna Sanata Uba Sani, da Mataimakin Gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa da Mataimakin Jagoran ’Yan Adawa na Majalisar Wakilai ta Kasa, Rt. Hon. Aliyu Sani Madaki.

An kuma samu halartar sarakuna da suka hada da Mai Martaba Sarkin Zazzau Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli da Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Adamu Abubakar Maje, wadanda suka bayar da gudummawa ta hikima da goyon baya a wajen taron.

A lokacin da yake gabatar da jawabi, Rt. Hon. Liman ya bayyana muradun al’ummar Kaduna dangane da batutuwan gyaran kundin tsarin mulki, inda ya jaddada bukatar sauya dokokin tsarin mulki domin su dace da zamani, da tabbatar da adalci, da daidaito da ingantaccen mulki.

“Gyaran kundin tsarin mulki na 1999 mataki ne mai muhimmanci wajen karfafa ginshikin dimokuraɗiyyar Najeriya. Jihar Kaduna za ta ci gaba da taka rawa wajen bada gudummawar gina tsarin mulki da zai kunshi kowa da kowa.” Inji shi. 

Taron jin ra’ayoyin na shiyyar Arewa yana ba da dama ga ’yan kasa, kungiyoyi da wakilan jama’a su bayyana ra’ayoyinsu da kuma gabatar da takardun bayani kan batutuwan kasa da suka shafe su.

Wannan wani muhimmin mataki ne na tabbatar da cewa tsarin gyaran kundin mulki yana tafiya ne bisa tsari mai kunshe da ra’ayin kowa da kowa daga sassa daban-daban na kasar.

 

Shamsuddeen Munnir Atiku 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Matsaya gyaran kundin tsarin mulki Jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Duk da cewa gwamnati na da dubban kwararrun malamai a makarantunta, har yanzu ana ganin ɗaliban makarantun gwamnati na kasa da na makarantun masu zaman kansu wajen ƙoƙari da kuma sakamakon jarabawa.

 

Wannan matsala ta daɗe tana jawo muhawara tsakanin iyaye, malamai da hukumomin ilimi.

Wasu na ganin matsaloli ne da ba za su rasa nasaba da rashin kulawa da watsi da harkar ilimi da gwamnati ta yi ba.

Ko wadanne dalilai ne suka daliban makarantun masu zaman kansu suka fi kokari idan aka kwatanta da daliban makarantu na gwamnati?

NAJERIYA A YAU: Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa PDP Ta Ki Sayarwa Sule Lamido Fom Din Takarar Shugaban Jam’iyya

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari