Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya gabatar da matsayar  Jihar Kaduna a zaman jin ra’ayin jama’a dangane da gyaran kundin tsarin mulkin shekarar 1999.

An gudanar da taron ne a gidan Gwamnati na General Hassan Katsina da ke Kawo, a garin Kaduna, a matsayin wani bangare na ci gaba da shirin gyaran kundin tsarin mulki da Majalisar Wakilai ta kasa ke jagoranta.

Wannan zaman jin ra’ayi da aka ware a matsayin Cibiyar ta daya, ya hada da jihohin Kaduna, Kano, Katsina da Jigawa.

Taron ya tara shugabanni daga fannoni daban-daban ciki har da ’yan siyasa, da sarakuna da kuma wakilan kungiyoyin fararen hula, domin tattauna batutuwan da suka shafi sauye-sauyen kundin tsarin mulki.

Cikin manyan bakin da suka halarci taron sun hada da Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Dr. Hadiza Balarabe, wacce ta wakilci Gwamna Sanata Uba Sani, da Mataimakin Gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa da Mataimakin Jagoran ’Yan Adawa na Majalisar Wakilai ta Kasa, Rt. Hon. Aliyu Sani Madaki.

An kuma samu halartar sarakuna da suka hada da Mai Martaba Sarkin Zazzau Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli da Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Adamu Abubakar Maje, wadanda suka bayar da gudummawa ta hikima da goyon baya a wajen taron.

A lokacin da yake gabatar da jawabi, Rt. Hon. Liman ya bayyana muradun al’ummar Kaduna dangane da batutuwan gyaran kundin tsarin mulki, inda ya jaddada bukatar sauya dokokin tsarin mulki domin su dace da zamani, da tabbatar da adalci, da daidaito da ingantaccen mulki.

“Gyaran kundin tsarin mulki na 1999 mataki ne mai muhimmanci wajen karfafa ginshikin dimokuraɗiyyar Najeriya. Jihar Kaduna za ta ci gaba da taka rawa wajen bada gudummawar gina tsarin mulki da zai kunshi kowa da kowa.” Inji shi. 

Taron jin ra’ayoyin na shiyyar Arewa yana ba da dama ga ’yan kasa, kungiyoyi da wakilan jama’a su bayyana ra’ayoyinsu da kuma gabatar da takardun bayani kan batutuwan kasa da suka shafe su.

Wannan wani muhimmin mataki ne na tabbatar da cewa tsarin gyaran kundin mulki yana tafiya ne bisa tsari mai kunshe da ra’ayin kowa da kowa daga sassa daban-daban na kasar.

 

Shamsuddeen Munnir Atiku 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Matsaya gyaran kundin tsarin mulki Jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Tana Nazarin Sakon Amurka Na Bukatar Farfado Da Tattaunawa Shirin Makamashin Nukliya Na kasar

Mai bawa jagoran Juyin Juya halin musulunci Imam Sayyid Ali Khamina’i, shawara Dr Ali Larijani ya bayyana cewa gwamnatin kasar Iran tana nazarin sakon gwamnatin Amurka na bukatar a farfado da tattaunawar shirin makamashin Nukliyar kasar tsakaninsu.

Kamfanin dillancin labaran Ip na kasar Iran ya nakalto Dr Larijana yana cewa gwamnatin kasar Iran tana shakkar Amurka a cikin duk abinda zai hada su musamman bayan yaki kwanaki 12 da ita Amurka da kuma HKI suka dora mata.

Dr Larijana ya fadawa tashar talabijin ta Aljazeera na kasar Qatar kan cewa, HKI da Amurka sun farwa kasar Iran da yaki ba tare da wani dalili ba, tana ma cikin tattaunawa da Ita kan shirin ta na makamas suka yi hakan. Suka kashe manya-manyan jami’an sojojin kasar da masana fasahar Nukliya da dama. Har’ila yau har da mutanen kasar Iran fararen hula suka kashe.

Ya ce HKI ta farwa yaki a ranar  13 watan Yunin shekara sannan amurka ta shiga a ranar 22 ga watan. Idan an hana wadannan duka da wasu da ban ambata ba, da sauki haka irin ba zata koma teburin tattaunawa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanatan Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC
  • Sanatar Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC
  • Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
  • Iran Tana Nazarin Sakon Amurka Na Bukatar Farfado Da Tattaunawa Shirin Makamashin Nukliya Na kasar
  • Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa
  • An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Wata Kungiya Mai Suna “Arewa Cohesion Initiative” Don Maganin Kalubalen Da Yankin Arewa Ke Fuskanta
  • Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo a Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo