Aminiya:
2025-09-17@21:51:43 GMT

Sanatar Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC

Published: 12th, July 2025 GMT

Sanata Ireti Kingibe, wacce ke wakiltar Babban Birnin Tarayya, ta fice daga jam’iyyar LP zuwa ADC.

Da ta ke magana da ’yan jarida a Abuja, ta ce wannan matakin nata wani shiri ne na tunkarar babban zaɓen 2027.

Abin da ya faru tsakani na da DSS bayan kama ni — Ɗan Bello DSS ta saki Ɗan Bello bayan ta kama shi a Kano

“Ni cikakkiyar mamba ce ta ADC yanzu,” inji ta.

Da aka tambaye ta ko tana da ƙwarin gwiwa game da shugabancin ADC da haɗin gwiwar da suke ƙoƙarin ginawa, ta ce jam’iyyar na ci gaba da samun tagomashi.

Tace kowace tafiya a sannu ake binta wanda daga bisani ta ke girma.

Wasu sun nuna damuwa cewa wannan sauya sheƙar na iya sawa ta rasa kujerarta a Majalisar Dattawa.

Amma Kingibe, ta ce jam’iyyar LP yanzu ta kasu gida biyu, wanda hakan ya sa ta bar jam’iyyar bisa ga kundin tsarin mulkin ƙasa.

Ta ce: “Ina roƙonku ku karanta kundin tsarin mulki. Akwai rarrabuwar kawuna a jam’iyyar LP, kuma wannan shi ne cikakken sharaɗi da kundin tsarin mulki ya bayar na yadda mutum zai iya sauya sheƙa ba tare da hukunci ba.”

“Idan kuna so na ci gaba da zama a jam’iyyar LP, wacce daga cikin ɓangarorin biyun kuke so na zauna a ciki?

“Har INEC sai da ta samu sakamakon zaɓe daga ɓangarori biyu na LP, kodayake ba su amince da kowane ba.”

Ta ƙara da cewa: “Ko da babu irin wannan rabuwar kan, kun taɓa ganin an tilasta wa wani barin kujerarsa?

“Amma ni ina bin doka. Da babu rabuwar kawuna a LP, da ba zan sauya sheƙa ba. Amma yanzu akwai, shi ya sa kundin tsarin mulki ya ba ni dama. Kuma na zaɓi ADC.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sauya Sheƙa kundin tsarin jam iyyar LP

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Matakin hana malaman da ba su da rajista hawa mumbari a Neja yana ci gaba da yamutsa hazo a ciki da wajen jihar.

Yayin da wasu suke ganin wannan mataki bai dace ba, wasu kuwa gani suke faduwa ta zo daidai da zama, wato matakin ya zo a daidai lokacin da ake bukata.

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kan tanadin Dokar Kasa game da wannan batu.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila