Sanatar Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC
Published: 12th, July 2025 GMT
Sanata Ireti Kingibe, wacce ke wakiltar Babban Birnin Tarayya, ta fice daga jam’iyyar LP zuwa ADC.
Da ta ke magana da ’yan jarida a Abuja, ta ce wannan matakin nata wani shiri ne na tunkarar babban zaɓen 2027.
Abin da ya faru tsakani na da DSS bayan kama ni — Ɗan Bello DSS ta saki Ɗan Bello bayan ta kama shi a Kano“Ni cikakkiyar mamba ce ta ADC yanzu,” inji ta.
Da aka tambaye ta ko tana da ƙwarin gwiwa game da shugabancin ADC da haɗin gwiwar da suke ƙoƙarin ginawa, ta ce jam’iyyar na ci gaba da samun tagomashi.
Tace kowace tafiya a sannu ake binta wanda daga bisani ta ke girma.
Wasu sun nuna damuwa cewa wannan sauya sheƙar na iya sawa ta rasa kujerarta a Majalisar Dattawa.
Amma Kingibe, ta ce jam’iyyar LP yanzu ta kasu gida biyu, wanda hakan ya sa ta bar jam’iyyar bisa ga kundin tsarin mulkin ƙasa.
Ta ce: “Ina roƙonku ku karanta kundin tsarin mulki. Akwai rarrabuwar kawuna a jam’iyyar LP, kuma wannan shi ne cikakken sharaɗi da kundin tsarin mulki ya bayar na yadda mutum zai iya sauya sheƙa ba tare da hukunci ba.”
“Idan kuna so na ci gaba da zama a jam’iyyar LP, wacce daga cikin ɓangarorin biyun kuke so na zauna a ciki?
“Har INEC sai da ta samu sakamakon zaɓe daga ɓangarori biyu na LP, kodayake ba su amince da kowane ba.”
Ta ƙara da cewa: “Ko da babu irin wannan rabuwar kan, kun taɓa ganin an tilasta wa wani barin kujerarsa?
“Amma ni ina bin doka. Da babu rabuwar kawuna a LP, da ba zan sauya sheƙa ba. Amma yanzu akwai, shi ya sa kundin tsarin mulki ya ba ni dama. Kuma na zaɓi ADC.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sauya Sheƙa kundin tsarin jam iyyar LP
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu
A wani rahoto da miami herald ya wallafa a jiya jumaa ya nuna cewa kasar Amurka na shirin kaiwa kasar Venuzuwela hare hare, yayin da Donald trump shugaban kasar Amurka yake musantawa cewa babu wani shiri na daukar matakin soji a kasar ta latin Amurka.
Yace gwamnatin trump ta yanke shawarar kai hari kan wasu wuraren soji a kasar, a kowanne lokaci.
Yace duk da yakin da washington ke yi kan miyagun kwayoyoi gwamnatinsa ba ta la’akari da kai hare-haren sojin kan venuzuwela yana nuna a akwai karo da juna a kalamansa na makon da ya gabata
Da manema labarai suka tambayeshi ko hare-haren da Amurka takai a yan kwanakin nan kan jiragen ruwa a yankin karebiya da aka ce suna fataucin miyagun kwayoyi na iya sanyawa akai hare hare kan venuzuwela trumpa ya amsa da cewa A’a.
A yan makwannin nan da suka gabata Trump ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta kai hari kan wuraren da suke da alaka da miyagun kwayoyi acikin venuzuwela yana mai cewa kasar za ta zama it ace ta gaba da za su daukai mataki a kanta.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci