Aminiya:
2025-07-23@04:59:57 GMT

Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa

Published: 22nd, July 2025 GMT

Jami’an tsaro sun hana Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da ’yan rakiyarta shiga haramar Majalisar Dokoki ta Kasa, inda ta je da niyyar halartar zaman Majlasiar Dattawa a ranar Talata.

Jami’an tsaro a daukacin kofofin shiga harabar majalisar sun hana ta shiga harabar majalisar ne a lokacin da ta yi yunkurin shiga domin halartar zaman ranar Talata, a yayin da magoya bayanta suka rako ta domin nuna goyon bayansu gare ta kan dakatarwar da majalisar ta yi mata.

A watan Maris ne da Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na tsawon wata shida kan zargin rashin da’a da kuma rashin bin tsarin wurin zaman da aka tanadar da mambobin majalisar a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2025.

A kana haka ne ’yar majalisar mai wakiltar Kogit ta Tsakiya ta garzaya Babbar Kotun Abuja, wadda ta umarci majalidar ta dawo da Sanata Natasha, bisa hujjar cewa majailsar ta wuce gona da iri wajen dakatar da ita har na tsawon wata shida.

Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati  An wajabta wa ɗaliban firamare mallakar lambar NIN a Bauchi

Alkalin kotu, Mai Shari’a Binta Nyako, ya bayyana cewa hukuncin da majalisar ta yanke ya yi tsauri da yawa, kuma ba shi da mazauni a doka.

Ta bayyana cewa doka na bukatar majalisar ta zauna sau 181 ne a shekara, kuma dakatarwar ta kusa tsawon wadanan kwanaki.

Ta ce hakan na nufin al’ummarta za su shafe kusan shekara guda ba tare mai wakiltans su ba a zauren majalisar, kuma ya saba da dokar kasa.

Tun loakcin Natasha ke ta kokarin komawa bakin aiki, inda a ranar Asabar ta lashi takobin halartar zama a ranar Talatar nan, idan majalisar ta dawo daga hutu.

Amma a ranar Litinin Shguaban Kwamitin Sadarwa na Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu ya fitar da sanarwa yana gargadin ta da cewa ya nisanci majalsiar.

Adaramodu ya yi ikirarin cewa Natasha ba ta cika umarnin kotu na biyan tarar Naira miliyan biyar ga Gwamnatin Tarayya kan kan raina kotu ba, da kuwa wallafa sakon neman afuwa a manyan jaridu biyu da kuma shafinta na Facebook.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: majalisar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.

A wani gagarumin mataki na karfafa yaki da rashin tsaro, gwamnatin jihar Zamfara ta gudanar da wani babban taron masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a Gusau, da nufin karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomi da kuma kaddamar da sabbin dabarun yaki da ayyukan ta’addanci da masu aikata laifuka.

 

Taron wanda aka gudanar a Sakatariyar JB Yakubu wanda ofishin sakataren gwamnatin jihar (SSG) ya shirya, ya hada manyan hafsoshin tsaro, manyan jami’an gwamnati, da wakilan hukumomin tarayya domin duba halin tsaro da jihar ke ciki.

 

A cewar wata sanarwa da babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga SSG, Suleman Ahmad Tudu, ya yi, an kira taron ne domin zurfafa hadin kai a tsakanin masu ruwa da tsaki domin kara inganta ayyukan da ake gudanarwa a fadin jihar.

 

Sakataren gwamnatin jihar, Malam Abubakar Nakwada, wanda ya jagoranci taron, daga bisani mataimakin gwamnan jihar, Mani Malam Mummuni, ya jadadda kudirin gwamnatin jihar na siyasa na maido da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

 

A cewar sanarwar, yayin taron, mahalarta taron sun tsunduma cikin wani muhimmin nazari kan kalubalen tsaro da ake fama da su tare da daukar sabbin shawarwari guda goma da gwamnatin jihar ta bullo da su.

 

Ta ce an tsara matakan ne don karfafa nasarorin da aka samu a baya-bayan nan da kuma kara kaimi wajen yaki da ‘yan fashi.

 

Da yake jawabi, Malam Nakwada ya yabawa jajircewa da sadaukarwar jami’an tsaro da ke aiki a fadin jihar Zamfara.

 

“Gwamnatin Jiha ta yaba da irin sadaukarwar da ku da manyan jami’an ku suka yi wajen kare lafiyar al’ummarmu, a madadin Mai Girma Gwamna Dauda Lawal, ina mika godiyarmu ga sadaukarwar da kuke yi ba tare da gajiyawa ba.” Inji shi.

 

SSG ya jaddada bukatar daidaitawa da dabarun hadin gwiwa wajen tinkarar barazanar da ke tasowa, inda ya bayyana cewa, hazaka, kirkire-kirkire, da hadin kai na ci gaba da zama muhimmi wajen samun zaman lafiya mai dorewa.

 

Ya kara da cewa, “domin tunkarar kalubalen tsaro masu sarkakiya yadda ya kamata, dole ne mu ci gaba da daidaitawa, yin sabbin abubuwa, da kuma yin aiki tare ba tare da wata matsala ba fiye da kowane lokaci.

 

Malam Nakwada ya kuma bayyana bakin cikinsa kan yawaitar hare-hare a sassan jihar, inda ya mika sakon ta’aziyyar gwamnati ga iyalai da al’ummomin da abin ya shafa.

 

“A madadin gwamnatin jihar Zamfara, ina jajantawa duk wadanda hare-haren baya-bayan nan ya rutsa da su, ina kuma tabbatar wa ‘yan kasa cewa ba za mu yi kasa a gwiwa ba har sai an samar da cikakken zaman lafiya a tsakanin kowace al’umma,” inji shi.

 

Ya kuma kara nanata kudirin Gwamna Dauda Lawal na samar wa jami’an tsaro kayan aiki, da tallafin da ake bukata domin fatattakar masu aikata miyagun laifuka da ke barazana ga zaman lafiya da tsaro a jihar Zamfara.

 

A nasa jawabin rufe taron mataimakin gwamna Mani Malam Mummuni ya yaba da gudunmawar da masu ruwa da tsaki suka bayar tare da yin kira da a kara himma da hadin kai.

 

“Muna matukar godiya da kokarin da aka yi ya zuwa yanzu, amma dole ne mu kara himma. Bari mu tabbatar da kowane inci na jihar mu da muke so mu maido da fata ga jama’armu,” in ji shi.

 

Taron dai wani mataki ne mai jajircewa da gwamnatin Dauda Lawal ta dauka na magance matsalolin tsaro a gaba, yayin da gwamnatin ke kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Zamfara.

 

REL/AMINU DALHATU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO
  • Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare
  • Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21
  • Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
  • Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro
  • Rayuwata Na Cikin Hatsari, A Dawo Min Da Jami’an Tsarona – Natasha 
  • Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne