Aminiya:
2025-09-17@23:19:36 GMT

Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa

Published: 22nd, July 2025 GMT

Jami’an tsaro sun hana Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da ’yan rakiyarta shiga haramar Majalisar Dokoki ta Kasa, inda ta je da niyyar halartar zaman Majlasiar Dattawa a ranar Talata.

Jami’an tsaro a daukacin kofofin shiga harabar majalisar sun hana ta shiga harabar majalisar ne a lokacin da ta yi yunkurin shiga domin halartar zaman ranar Talata, a yayin da magoya bayanta suka rako ta domin nuna goyon bayansu gare ta kan dakatarwar da majalisar ta yi mata.

A watan Maris ne da Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na tsawon wata shida kan zargin rashin da’a da kuma rashin bin tsarin wurin zaman da aka tanadar da mambobin majalisar a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2025.

A kana haka ne ’yar majalisar mai wakiltar Kogit ta Tsakiya ta garzaya Babbar Kotun Abuja, wadda ta umarci majalidar ta dawo da Sanata Natasha, bisa hujjar cewa majailsar ta wuce gona da iri wajen dakatar da ita har na tsawon wata shida.

Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati  An wajabta wa ɗaliban firamare mallakar lambar NIN a Bauchi

Alkalin kotu, Mai Shari’a Binta Nyako, ya bayyana cewa hukuncin da majalisar ta yanke ya yi tsauri da yawa, kuma ba shi da mazauni a doka.

Ta bayyana cewa doka na bukatar majalisar ta zauna sau 181 ne a shekara, kuma dakatarwar ta kusa tsawon wadanan kwanaki.

Ta ce hakan na nufin al’ummarta za su shafe kusan shekara guda ba tare mai wakiltans su ba a zauren majalisar, kuma ya saba da dokar kasa.

Tun loakcin Natasha ke ta kokarin komawa bakin aiki, inda a ranar Asabar ta lashi takobin halartar zama a ranar Talatar nan, idan majalisar ta dawo daga hutu.

Amma a ranar Litinin Shguaban Kwamitin Sadarwa na Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu ya fitar da sanarwa yana gargadin ta da cewa ya nisanci majalsiar.

Adaramodu ya yi ikirarin cewa Natasha ba ta cika umarnin kotu na biyan tarar Naira miliyan biyar ga Gwamnatin Tarayya kan kan raina kotu ba, da kuwa wallafa sakon neman afuwa a manyan jaridu biyu da kuma shafinta na Facebook.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: majalisar ta

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya DSS, ta gurfanar da fitaccen ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore a kotu.

A ƙunshin ƙarar da DSS ta gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da shafukan sada zumunta na X da kuma Facebook, inda take zarginsu da ba da ƙofar aibata Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku

Darekan shigar da ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, M.B Abubakar da wasu lauyoyi huɗu —M.E. Ernest da U.B. Bulla da C.S. Eze da kuma E.G. Orubor, ne suka shigar da ƙarar a madadin Gwamnatin Tarayya da kuma hukumar ta DSS.

DSS wadda ta kafa hujja da sashe na 24 da ke cikin kundin dokokin yanar gizo, ta ce Sowore ya yi amfani da shafukansa na dandalan sada zumunta na X da Facebook wajen wallafa wani saƙo da ke cin mutuncin Shugaba Tinubu.

Tun dai a farkon watan nan ne DSS ta buƙaci goge wani saƙo da ɗan gwagwarmayar ya wallafa wanda ta riƙa a matsayin bayanan ƙarya, cin zarafi ta yanar gizo da kalaman haddasa ƙiyayya, waɗanda kuma ta ce na iya haddasa rikici su kuma ɓata sunan Najeriya a ƙasashen waje.

Sai dai har zuwa ranar Litinin, 15 ga watan Satumba, babu wani mataki da aka ɗauka na goge saƙon da DSS ɗin ta buƙata.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin