Aminiya:
2025-07-25@14:16:25 GMT

Mahajjata kusan miliyan biyu na hawan Arfa a Saudiyya

Published: 5th, June 2025 GMT

Miliyoyin alhazai ciki har da ’yan Najeriya ne suka taru a Dutsen Arfa domin tsayuwa a yayin Aikin Hajjin bana duk da tsananin zafin ranar da ake fama da shi a kasar Saudiyya.

Ministan Aikin Hajji na kasar dai ya shawarci mahajjatan da su kasance a cikin tantinansu tun daga tsakain karfe 10 na safe zuwa karfe 4:00 na yamma, saboda tsananin zafin rana.

Ko a ranar Lahadi sai da Hukumar Hasashen Yanayi ta Kasar (NCM) ta yi gargadin cewa zafin zai iya kai wa ma’auni 47, inda ta shawarce su da su dauki matakan kariya.

Musulman Kudancin Kaduna sun yi taron addu’ar zaman lafiya Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano

To sai dai duk da haka, mahajjata maza da mata sun rika yin tattaki daga wurare masu nisa domin taruwa a dutsen domin yin addu’a.

Da yake zantawa da wakilinmu, daya daga cikin mahajjatan Najeriya, Yusuf Hassan, cewa yana sane da shawarar da aka bayar, amma duk da haka zuciyarsa ba za ta iya natsuwa ba sai yah au dutsen na rahama.

“Na yi wa kaina alkawarin cewa sai nah au Dutse Arafat na yi addu’a a duk lokacin da Allah y aba ni dama. Saboda haka ni burina ya cika,” in ji shi.

Sai dai wakilin namu ya shaida cewa akasarin mahajjatan sun yi amfani da shawarar, inda suka tsaya a cikin tantinan nasu suna karatun alkur’ani da salloli da addu’o’i.

Kazalika, wakilin namu ya ce ya hangi jirage masu saukar angulu na shawagi a sararin samaniya, yayin da ’yan sanda da sauran jami’an tsaro ke ci gaba da sintiri suna yi wa mahajjatan jagora.

Dutse Arafat dai na da tarihi sosai a Musulunci saboda a nan ne tarihi ya nuna Annabi Muhammad (S.A.W) ya gudanar da hudubarsa ta bankwana.

Daga dutsen ne kuma za su koma Muzdalifa da yamma, su kwana a can, kashegari da safe kuma su fara jifan Shedan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Arfa Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana

Alkaluma da aka fitar a hukumance sun nuna cewa, kasar Sin ta samar da sabbin guraben aikin yi miliyan 6.95 a rabin farko na bana, inda ta cimma kaso 58 bisa dari na burinta na shekara.

Kakakin ma’aikatar kula da ma’aikata da walwalar al’umma ta kasar Sin Cui Pengcheng ne ya bayyana haka yayin wani taron manema labarai a yau Talata, inda ya ce a watan Yuni, yawan wadanda ba su da aiki a birane ya tsaya kan kaso 5 bisa dari, watau bai sauya ba daga yadda ya kasance shekara 1 da ya wuce.

Kasar Sin na da burin adadin marasa aikin yi ya tsaya kan kaso 5.5 a bana, tare da burin samar da guraben aikin yi sama da miliyan 12. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Ke Fuskantar Barazanar Kwararowar Hamada – Ministan Muhalli
  • Yan Majalisar Dokokin Kasashen Iran Da Iraki Sun Amince Da Ra’yin Ficewar Sojojin Amurka Daga Iraki
  • Tinubu ya sake miƙa buƙatar karɓo bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare
  • WFP zai dakatar da tallafin abinci da kiwon lafiya a Nijeriya
  • Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana
  • Hisbah Ta Lalata Barasa Ta Naira Miliyan 5.8 A Jigawa