Mahajjata kusan miliyan biyu na hawan Arfa a Saudiyya
Published: 5th, June 2025 GMT
Miliyoyin alhazai ciki har da ’yan Najeriya ne suka taru a Dutsen Arfa domin tsayuwa a yayin Aikin Hajjin bana duk da tsananin zafin ranar da ake fama da shi a kasar Saudiyya.
Ministan Aikin Hajji na kasar dai ya shawarci mahajjatan da su kasance a cikin tantinansu tun daga tsakain karfe 10 na safe zuwa karfe 4:00 na yamma, saboda tsananin zafin rana.
Ko a ranar Lahadi sai da Hukumar Hasashen Yanayi ta Kasar (NCM) ta yi gargadin cewa zafin zai iya kai wa ma’auni 47, inda ta shawarce su da su dauki matakan kariya.
Musulman Kudancin Kaduna sun yi taron addu’ar zaman lafiya Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a KanoTo sai dai duk da haka, mahajjata maza da mata sun rika yin tattaki daga wurare masu nisa domin taruwa a dutsen domin yin addu’a.
Da yake zantawa da wakilinmu, daya daga cikin mahajjatan Najeriya, Yusuf Hassan, cewa yana sane da shawarar da aka bayar, amma duk da haka zuciyarsa ba za ta iya natsuwa ba sai yah au dutsen na rahama.
“Na yi wa kaina alkawarin cewa sai nah au Dutse Arafat na yi addu’a a duk lokacin da Allah y aba ni dama. Saboda haka ni burina ya cika,” in ji shi.
Sai dai wakilin namu ya shaida cewa akasarin mahajjatan sun yi amfani da shawarar, inda suka tsaya a cikin tantinan nasu suna karatun alkur’ani da salloli da addu’o’i.
Kazalika, wakilin namu ya ce ya hangi jirage masu saukar angulu na shawagi a sararin samaniya, yayin da ’yan sanda da sauran jami’an tsaro ke ci gaba da sintiri suna yi wa mahajjatan jagora.
Dutse Arafat dai na da tarihi sosai a Musulunci saboda a nan ne tarihi ya nuna Annabi Muhammad (S.A.W) ya gudanar da hudubarsa ta bankwana.
Daga dutsen ne kuma za su koma Muzdalifa da yamma, su kwana a can, kashegari da safe kuma su fara jifan Shedan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hawan Arfa Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.
A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan NejaYa bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.
Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.
Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.
TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.
Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”
Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.
Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.
Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.