Aminiya:
2025-07-12@12:29:19 GMT

Ɗalibi ya ƙone budurwarsa mai tsohon ciki har lahira

Published: 12th, July 2025 GMT

Ana zargin wani ɗalibi da ke shekarar ƙarshe a jami’a da ƙona budurwarsa mai ɗauke da tsohon ciki a Jami’ar Fatakwal da ke Jihar Ribas.

Wanda ake zargin da budurwar tasa mai suna Cynthia Chukwundah, dukkansu ɗaliban ajin ƙarshe ne a jami’ar.

Ana zargin matashin ya ƙona Cynthia mai shekara 32 ne ta hanyar wata mata ruwan batir, daga bisani ta ce ga garinku nan.

Cynthia ta gamu da ajalinta ne bayan saurayinta Sunny Amadi ya yi mata wannan aika-aika a gidansu da ke layin Okoro unguwar China da ke Birnin Fatakwal.

Sojoji sun kama mai garkuwa da mutane da bindigogi Muna tunanin sayar da matatun man Najeriya — NNPCL

Wani ganau da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa Aminiya cewa “Abu kamar wasa suka fara cacar baki, wannan na faɗa wannan na mayar da martani kowa dai bai sanya musu baki ba, kowa kuma ya shiga ɗakinsa ya kwanta. Ƙarshe sai ya watsa mata wani sinadarin da ya ƙone ta kamar ƙunar wuta, ga ta ɗauke da tsohon ciki, ita da tsohon ciki da abin da ke cikin cikin suka mutu,” in ji majiyar.

Ya ce, “Bayan da saurayin ya yi wa Cynthia wannan aika-aika, ya sulale ya gudu, amma daga baya ’yan sanda suka kama shi a maɓoyarsa.

“Maƙwabta suka yi ƙoƙarin gaggawar kai ta Asibitin Koyarwa na Jami’ar Fatakwal (UPTH ) domin a ceto rayuwarta da ta abin da ke cikin cikinta, amma rai ya yi halinsa sakamakon munanan raunuka na sinadarin da saurayin ya watsa mata a jiki da ake zato sinadarin Asid ne.”

Kakakin ’yan sanda a Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana cewa rundunar tana tsare da saurayin kuma yana bayar da haɗin kai a binciken da ke gudanarwa, kuma da zarar an kammala bincike, za a miƙa shi kotu ta yi aikinta.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Ya Kakabawa Wata Jami’in MDD Takunkumi Bayan Ta Fallasa Laifukan HKI Da Hannun Amurka A Ciki

Gwamnatin kasar Amurka ta dorawa wata ma’aikaciyar MDD takunkumi saboda yadda take amfanin laifukan yaki da take yi a gaza da kuma irin tallafin da Amurka take bawa HKI yasa tana da hannun a kissan kiyashin.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa sakataren harkokin wajen kasar Amurka Marco Rubio ya bayyana cewa shi ya sa hannu a kan umurnin takunkuman da aka dorawa Francesa Albanese, jami’a mai kula da tattara bayanai na musamman a kan Falasdinu ga hukumar kare hakkin bil’dama da MDD.

Rubio ya bayyana cewa sanadiyyar rahoton ta ne kotun ICC ta fidda samacin kama Banyamin Natanyaho, da kuma tsohon ministansa na Tsaro Yoav Galant. Banda haka takan bada rahoto kan yadda Amurka da wasu kasashen yamma suke aikawa HKI makamai.

Sannan ya ce: Albanese tana yawan amfani da Kalmar kissan kiyashi a rahotonta. A watan da ya gabata ta bukaci a sanyawa HKI takunkuman tattalin arziki mai tsanani. A wani lokacin kuma ta bukaci majalisar ta kori HKI daga MDD.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Direba ya tsere da buhun masara 463
  • Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana
  • An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba
  • An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 22 Kan Zargin Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato
  • Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawa
  • Trump Ya Kakabawa Wata Jami’in MDD Takunkumi Bayan Ta Fallasa Laifukan HKI Da Hannun Amurka A Ciki
  • Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II