Jami’an ‘yan sanda da suka yi ritaya a jihar Kwara sun gudanar da zanga-zangar lumana don neman a cire su daga shirin bayar da gudunmawar fansho (CPS).

 

An ga jami’an ‘yan sandan da suka yi ritaya a jihar karkashin kungiyar ‘yan sandan Najeriya mai ritaya (ARPON), dauke da kwalaye masu rubuce-rubuce daban-daban kamar su “Shugaban kasa, NASS da IGP ya kamata a girmama ‘yan sanda su kebe ‘yan sanda daga CPS, su kafa hukumar ‘yan sanda ta fensho don gudanar da gratuity da fansho, idan CPS na da kyau haka, me ya sa AIGs da sauran su suka fice daga cikin shirin?

 

Da yake jawabi ga ‘ya’yan kungiyar a lokacin zanga-zangar lumana a Ilorin, shugaban kungiyar, Yakubu Jimoh, babban Sufeton ‘yan sanda mai ritaya, ya yi zargin cewa shirin yana cike da kalubale tun farkonsa.

 

A cewarsa jami’an da suka yi ritaya wadanda suka fada cikin tsarin fansho ya kamata a kebe su kamar wadanda suka kai matsayin Janar a rundunar.

 

Ya nemi kafa hukumar fansho ta ‘yan sanda mai alhakin kula da al’amuran ‘yan sanda na fansho kamar yadda ya shafi sauran hukumomin tsaro.

 

Jimoh ya bayyana cewa rahoton kwamitin majalisar dattijai mai kula da kafa da ayyukan gwamnati a kan kudirin dokar kafa hukumar fansho ta ‘yan sanda, wadda aka gudanar a watan Nuwambar bara ta fitar da shi, duk da cewa an gudanar da shi watanni takwas da suka gabata.

Ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da majalisar dokokin kasar da su gaggauta bin diddigin yadda majalisar za ta bi wajen fitar da naira biliyan 758, karancin kudaden fansho da ke bin hukumomin tsaro.

 

A nasa bangaren, mashawarcin shari’a na kungiyar ‘yan sandan Najeriya mai ritaya Adekunle Iwalaiye, ya ce jami’an da suka yi ritaya sun cancanci a biya su fansho na rayuwa ba wai dan abin da ake jefa musu ba duk wata ba.

 

Ya bukaci gwamnati da ta yi aiki da bukatar wadanda suka yi ritaya, duba da irin ayyukan alheri da suka yi wa kasar nan tsawon shekaru 35.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara Yansanda da suka yi ritaya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

 

Haka kuma, wannan na faruwa ne makonni biyu bayan yin garkuwa da Pastor Friday Adehi na Christian Evangelical Fellowship of Nigeria (CEFN) tare da wani abokin cocinsa bayan kammala wa’azi. Wannan ya kara nuna yadda matsalar garkuwa ke ta’azzara a yankin Kogi East.

 

A gefe guda, kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA), reshen Idah, ta bukaci gwamnati a matakai daban-daban da ta dauki matakan gaggawa don kawo karshen satar mutane a jihar. Shugaban kungiyar, Barr. James Michael, ya ce yawaitar garkuwa a kan titunan yankin ya jefa rayukan jama’a cikin hatsari, don haka gwamnati ya kamata ta dauki tsauraran matakai domin kare lafiyar al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Runduwar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin