Jami’an ‘yan sanda da suka yi ritaya a jihar Kwara sun gudanar da zanga-zangar lumana don neman a cire su daga shirin bayar da gudunmawar fansho (CPS).

 

An ga jami’an ‘yan sandan da suka yi ritaya a jihar karkashin kungiyar ‘yan sandan Najeriya mai ritaya (ARPON), dauke da kwalaye masu rubuce-rubuce daban-daban kamar su “Shugaban kasa, NASS da IGP ya kamata a girmama ‘yan sanda su kebe ‘yan sanda daga CPS, su kafa hukumar ‘yan sanda ta fensho don gudanar da gratuity da fansho, idan CPS na da kyau haka, me ya sa AIGs da sauran su suka fice daga cikin shirin?

 

Da yake jawabi ga ‘ya’yan kungiyar a lokacin zanga-zangar lumana a Ilorin, shugaban kungiyar, Yakubu Jimoh, babban Sufeton ‘yan sanda mai ritaya, ya yi zargin cewa shirin yana cike da kalubale tun farkonsa.

 

A cewarsa jami’an da suka yi ritaya wadanda suka fada cikin tsarin fansho ya kamata a kebe su kamar wadanda suka kai matsayin Janar a rundunar.

 

Ya nemi kafa hukumar fansho ta ‘yan sanda mai alhakin kula da al’amuran ‘yan sanda na fansho kamar yadda ya shafi sauran hukumomin tsaro.

 

Jimoh ya bayyana cewa rahoton kwamitin majalisar dattijai mai kula da kafa da ayyukan gwamnati a kan kudirin dokar kafa hukumar fansho ta ‘yan sanda, wadda aka gudanar a watan Nuwambar bara ta fitar da shi, duk da cewa an gudanar da shi watanni takwas da suka gabata.

Ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da majalisar dokokin kasar da su gaggauta bin diddigin yadda majalisar za ta bi wajen fitar da naira biliyan 758, karancin kudaden fansho da ke bin hukumomin tsaro.

 

A nasa bangaren, mashawarcin shari’a na kungiyar ‘yan sandan Najeriya mai ritaya Adekunle Iwalaiye, ya ce jami’an da suka yi ritaya sun cancanci a biya su fansho na rayuwa ba wai dan abin da ake jefa musu ba duk wata ba.

 

Ya bukaci gwamnati da ta yi aiki da bukatar wadanda suka yi ritaya, duba da irin ayyukan alheri da suka yi wa kasar nan tsawon shekaru 35.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara Yansanda da suka yi ritaya

এছাড়াও পড়ুন:

 Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta

Kungiyar kwallon kafa ta Iran ta aike da sako zuwa ga hukumar kwallon kafa ta duniya da ta kori HKI daga cikinta

Shugaban kungiyar kwallon kafa ta Iran Mahdi Taj, ya bayyana cewa: Mun yi kira ga Sheikh Salman akan daukar kwakkwaran mataki akan ‘Yan Sahayoniya. Mun kuma rubuta wasika zuwa ga Fifa akan cewa ya zama wajibi a dagawa HKI jan kati.

 Bugu da kari, ya kuma ce; “Yan sahayoniya sun kai wa hukumar kwallon kafa ta Iran hari, ta kuma kashe mana alkalai, ‘yan wasa, don haka ya zama wajibi a kore su daga  Fifa.

 Taj ya kuma ce; Mun sami ci gaba sosai a wannan fagen, muna fatan kungiyar Fifa ta yi la’akari da wadannan laifukan na Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Hisba Ta Jihar Jigawa
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  •  Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
  • PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu
  • Gwamna Radda Da Makarrabansa Na Samun Kulawa A Asibiti Bayan Hatsarin Mota A Hanyar Daura
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi