Dan majalisa mai wakiltar mazabar Katagun ta tarayya a jihar Bauchi Alh. Awwalu Abdu Gwalabe, ya bayar da hujjar cewa tattalin arzikin Najeriya na da karfin da zai iya dorewar karin jihohi 12.

 

Ya bayyana haka ne ga manema labarai a wajen taron jin ra’ayin jama’a kan sake duba kundin tsarin mulkin 1999 a Arewa maso Gabas a Gombe

 

Alh.

Awwalu Gwalabe, ya ci gaba da cewa, idan har Gwamnatin Tarayya za ta iya kashe Naira tiriliyan 17 wajen gina titin lagos-calabar kadai, hakan na nuni da cewa tattalin arzikin zai iya dorewar samar da karin jihohi.

 

Ya ce sama da shekaru arba’in ne al’ummar shiyyar katagun a jihar Bauchi suke ta tada jijiyoyin wuya na ganin an samar da jiha amma tsarin mulki da sauran cikas ya hana su yunkurin cimma burinsu.

 

Dan majalisar ya yi watsi da ikirarin cewa da wuya a samar da karin jihohi a tsarin dimokuradiyya saboda matsalolin da kundin tsarin mulkin kasar ya tanada a cikin tsarin ya ce kawai yana bukatar a sauya wani sashe na Kundin Tsarin Mulki domin a samu sauki.

 

A cewarsa idan aka gyara bangaren kundin tsarin mulkin kasar da ya amince da kasancewar jihohi 36 da FCT za a iya gyara wanda zai samar da wata hanya ta samar da karin jihohi.

 

Alh. Awwal Gwalabe ya roki al’ummar shiyyar Katagun da ke jihar Bauchi da kada su karaya, su ci gaba da tara wakilansu a zauren majalisar dokokin kasar domin jihar Katagun ta tabbata.

 

HUDU/Gombe

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: samar da karin jihohi

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Taya Super Eagles Murnar Samun Cancantar Shiga Gasar Kwallon Kafa Ta Duniya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya kungiyar kwallon kafa ta kasaSuper Eagles murnar nasarar da suka samu ta ci 4 da nema a kan Cheetahs ta Jamhuriyar Benin, tare da yabawa ƙungiyar bisa ƙoƙarin da take yi na ci gaba da kokarin cika al’umma, yayin da suke neman cancantar zuwa gasar cin Kofin Duniya ta FIFA a shekarar 2026.

Shugaban ƙasar ya jinjina wa Super Eagles bisa ƙwazo, da jajircewar da suka nuna a filin wasa na Uyo, yana mai cewa wannan gagarumar nasarar ta sake karfafa ‘yan Najeriya kan harkar ƙwallon ƙafa.

“Yanayin farin ciki da ake ciki a fadin ƙasar nan na nuni da yakinin da muke da shi  cewa Najeriya ta cancanci samun gurbi a gasar Kofin Duniya ta 2026, wadda Kanada, da Mexico, da Amurka za su karɓi bakunci.”

“A matsayina na Shugaban ƙasa, ina tabbatar muku  da cikakken goyon bayan Gwamnatin Tarayya, yayin da kuke ƙoƙarin tabbatar da gurbin ku a gasar.

Hakazalika ‘yan Najeriya na da yakinin cewa za ku yi nasara, ni ma haka.”

“Muna sa ran ganin ku kuna daga tutar Najeriya cikin alfahari a matakin duniya.” Inji Shi.

Daga Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump Ya Fadawa Hamas Su Mika Makamansu Ko Kuma A Kwace Su Da Karfi
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Super Eagles Murnar Samun Cancantar Shiga Gasar Kwallon Kafa Ta Duniya
  • Araghchi : Trump bai cancanci mai samar da zaman lafiya ba yayin da yake haifar da yake-yake
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya
  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje