Tattalin Arzikin Najeriya Na Da Karfi Samar Da Karin Jihohi. Inji Dan Majalisa.
Published: 13th, July 2025 GMT
Dan majalisa mai wakiltar mazabar Katagun ta tarayya a jihar Bauchi Alh. Awwalu Abdu Gwalabe, ya bayar da hujjar cewa tattalin arzikin Najeriya na da karfin da zai iya dorewar karin jihohi 12.
Ya bayyana haka ne ga manema labarai a wajen taron jin ra’ayin jama’a kan sake duba kundin tsarin mulkin 1999 a Arewa maso Gabas a Gombe
Alh.
Ya ce sama da shekaru arba’in ne al’ummar shiyyar katagun a jihar Bauchi suke ta tada jijiyoyin wuya na ganin an samar da jiha amma tsarin mulki da sauran cikas ya hana su yunkurin cimma burinsu.
Dan majalisar ya yi watsi da ikirarin cewa da wuya a samar da karin jihohi a tsarin dimokuradiyya saboda matsalolin da kundin tsarin mulkin kasar ya tanada a cikin tsarin ya ce kawai yana bukatar a sauya wani sashe na Kundin Tsarin Mulki domin a samu sauki.
A cewarsa idan aka gyara bangaren kundin tsarin mulkin kasar da ya amince da kasancewar jihohi 36 da FCT za a iya gyara wanda zai samar da wata hanya ta samar da karin jihohi.
Alh. Awwal Gwalabe ya roki al’ummar shiyyar Katagun da ke jihar Bauchi da kada su karaya, su ci gaba da tara wakilansu a zauren majalisar dokokin kasar domin jihar Katagun ta tabbata.
HUDU/Gombe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: samar da karin jihohi
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Taya Super Eagles Murnar Samun Cancantar Shiga Gasar Kwallon Kafa Ta Duniya
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya kungiyar kwallon kafa ta kasaSuper Eagles murnar nasarar da suka samu ta ci 4 da nema a kan Cheetahs ta Jamhuriyar Benin, tare da yabawa ƙungiyar bisa ƙoƙarin da take yi na ci gaba da kokarin cika al’umma, yayin da suke neman cancantar zuwa gasar cin Kofin Duniya ta FIFA a shekarar 2026.
Shugaban ƙasar ya jinjina wa Super Eagles bisa ƙwazo, da jajircewar da suka nuna a filin wasa na Uyo, yana mai cewa wannan gagarumar nasarar ta sake karfafa ‘yan Najeriya kan harkar ƙwallon ƙafa.
“Yanayin farin ciki da ake ciki a fadin ƙasar nan na nuni da yakinin da muke da shi cewa Najeriya ta cancanci samun gurbi a gasar Kofin Duniya ta 2026, wadda Kanada, da Mexico, da Amurka za su karɓi bakunci.”
“A matsayina na Shugaban ƙasa, ina tabbatar muku da cikakken goyon bayan Gwamnatin Tarayya, yayin da kuke ƙoƙarin tabbatar da gurbin ku a gasar.
Hakazalika ‘yan Najeriya na da yakinin cewa za ku yi nasara, ni ma haka.”
“Muna sa ran ganin ku kuna daga tutar Najeriya cikin alfahari a matakin duniya.” Inji Shi.
Daga Bello Wakili